ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

by Sani Anwar and Sulaiman
9 months ago
Kwalara

Kimanin mutum 4,778 ne suka mutu sakamakon kamuwa da cutar Kwalara a Nijeriya, tsakanin shekarar 2020 zuwa 2024, kamar yadda bayanai daga cibiyar yaki da cututtuka ta Nijeriya (NCDC) ta bayyana.

 

A cikin wannan shekarar kadai, an samu rahoton mutuwar sama da mutum 300, ciki har da wasu mace-macen na mutum 179; a cewar wata sanarwa da Gwamnatin Jihar Zamfara ta fitar a karshen mako, daga cikin mutum 12,052 da ake zargin sun kamu da cutar a jihar ya zuwa watan Satumbar 2025.

ADVERTISEMENT
  • An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 
  • Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

Makwanni biyu da suka gabata, Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi, Auwal Mohammed Jatau, ya tabbatar da samun sabbin mutane 58 da suka mutu daga wasu sabbin mutane 258 da suka kamu da cutar a fadin kananan hukumomi 14 na jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

Yawan mace-mace ta hanyar cutar kwalarar, na faruwa ne duk da biliyoyin Nairori da aka ce gwamnati da abokan huldar kasa da kasa suna kashewa, domin kokarin ganin an dakile ta.

 

Wadannan kudade sun hada da kason kasafin kudi na shekara-shekara, wanda ya kunshi miliyoyin Nairori; akwai dala miliyan 700 da bankin duniya ya bayar domin samar da tsaftataccen ruwa sha, tsaftar muhalli a fadin kasa baki-daya, tallafin dala miliyan 2 daga Majalisar Dinkin Duniya, dubban daruruwan allurar rigakafin cutar kwalara da asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) suka bayar da sauran makamantansu.

Alkaluman da aka samu daga cibiyar NCDC, sun nuna cewa a cikin 2020, kasar ta samu rahoton kimanin mutane 3,513 da ake zargi da kamuwa da cutar da kuma mutuwar mutum 95. Adadin wadanda suka mutu ya karu kwarai da gaske a shekarar 2021 tare da mutum 111,062 da ake zargi da kamuwa da cutar, kazalika akwai mutum 3,604 da suka mutu a cikin jihohi 33, ciki har da babban birnin tarayya Abuja.

Har ila yau, kwayar cutar kwalara ta ‘Bibrio cholerae’ ce ta haifar da ita, cutar kwalara cuta ce da ake saurin kamuwa da ita; ta hanyar gurbataccen abinci da ruwa da kuma rashin tsaftar muhalli ke haifar da ita.

Barkewar cutar, ta fi yin kamari a lokacin damina, daga watan Mayu zuwa watan Oktoba, yayin da ambaliyar ruwa da gurbatattun hanyoyin ruwa ke kara ta’azzara wajen yaduwa. Alamomin cutar kwalara sun hada da yawan zawo, amai da murdawar ciki da kuma rashin ruwa a jiki. Za kuma a iya saurin tarar cutar ta hanyar amfani da ruwan gishi da sikari da kuma rigakafi, idan ba a yi saurin aiwatar da hakan ba, za a iya rasa rai cikin kankanin lokaci.

Shekarar 2021 na daya cikin wadda ake zargin mutane kimanin 111,062, sun kamu da cutar tare da mutuwar kusan mutum 3,604 a jihohi 33 ciki har da babban birnin tarayya Abuja tare da yara ‘yan shekara daga 5 zuwa 14 da suka fi kamuwa da cutar.

Jihohin Bauchi, Jigawa, Kano da Zamfara ne ke da kashi 53 cikin 100 na dukkanin masu fama da cutar.

A shekarar 2022, alkaluman yawan mace-macen sun ragu zuwa 592, wato da kashi 2.5 cikin 100, kazalika a cikin 23,763 da ake zargi sun kamu da cutar daga jihohi 32 ciki har da babban birnin tarayya Abuja, Jihohin Borno, Yobe, Katsina, Gwambe, Taraba da Kano, na da kashi 83 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar.

Daga cikin mutum 3,683 da ake zargin sun kamu da wannan cuta ta kwalara a 2023 a cikin jihohi 31, an samu rahoton mutuwar mutum 128 (kashi 3.5 cikin 100), inda yara ‘yan kasa da shekara biyar suka fi kamuwa da cutar, sai kuma wadanda ke tsakanin shekaru biyar zuwa 14. Jihar Zamfara ce ke da kashi 25 cikin 100 na dukkanin wadanda ake zargi da kamuwa; yayin da Jihohin Kuros Riba, Katsina, Bayelsa, Ogun, Ebonyi da kuma Neja ke da kashi 57 cikin 100.

Adadin ya sake karuwa a shekarar 2024 zuwa mutum 10,837 da ake zargin sun kamu da cutar da kuma mutuwar mutane 359 deaths (kashi 3.3 cikin 100) a fadin jihohi 36 na kasar nan a ranar 29 ga watan Satumba, wanda shi ne na karshe da cibiyar NCDC ta fitar kan bullar cutar ta kwalara a wannan shekarar. Har ila yau, yara ‘yan kasa da shekara biyar sun fi kamuwa da cutar, sai kuma wadanda ke tsakanin shekara biyar zuwa 14. Kazalika, Jihar Legas ta samu kashi 43 cikin 100 na kafatanin wadanda ake zargi da kamuwa da cutar.

A cikin watan Yulin bana, yayin da aka kaddamar da neman tallafin gaggawa na kimanin dala miliyan 20, domin yaki da cutar kwalara a Nijeriya da sauran kasashen yammacin Afirka da kuma Afirka ta tsakiya, daraktan yanki na UNICEF, Gilles Fagninou ya ce; “Zuwa karshen watan Yuni, Nijeriya ta samu rahoton bullar cutar kwalara kimanin 3,109 da kuma mutuwar mutum 86 cikin jihohi 34.”

Ya ce, yawan adadin wadanda ake zargin sun kamu da cutar ne yasa Nijeriya ta kasance a matsayin kasa ta biyu da cutar ta fi yin kamari a yammacin Afirka da kuma Afirka ta tsakiya.

Ya kara da cewa, “Mamakon ruwa da ambaliyar ruwan sama da kuma yawan wadanda suka rasa matsugunansu, duk suna kara ruruta wutar hadarin kamuwa da cutar kwalara da kuma jefa rayuwar yara cikin hadari. Yara kanana, sun fi fuskantar barazanar kamuwa da cutar kwalara, sakamakon dalilai kamar haka; rashin tsafta, rashin samun tsaftataccen ruwa sha, rashin tsaftace muhalli da kuma rashin isasshen ruwa a jikin mutum,” in ji shi.

 

Yadda Muka Rasa Su Cikin Kankanin Lokaci- Iyalai

Wata fita da matar Musa Aliyu ta yi da ‘ya’yanta uku cikin farin ciki, ta kare bakin ciki da kuka ga ‘yan’uwa; bayan halartarsu wani bikin daurin aure a unguwar da ke makwabtaka da cikin birnin Bauchi. Bayan ‘yan sa’o’i kadan da kammala cin abinci a wajen taron, sai suka fara amai da bayan gida a-kai-a-kai.

“Matata da ‘ya’yana uku, sun kamu da cutar bayan cin abinci a wajen wani wurin daurin aure a Bauchi, ‘yata ta farko ce ta fara kamuwa; kafin daga bisani sauran ‘ya’yan nawa biyu suka kamu da kuma mahaifiiyarsu,” wani mazaunin ‘Federal Low Cost Housing Estate’.

Duk da cewa, wasu daga cikinsu sun tsira da rayukansu; amma Muhammad Aliyu, mai shekaru 5 ya rasu. Yanzu haka, shekara hudu kenan da rasuwarsa, amma mutuwar tasa ta bar tabon dab a zai taba gogewa ba a dangin.

A shekarar 2021 a Bauchin, cutar ta yi wa ‘ya’yan Fatima su bakwai yankan kauna, wadanda mahaifinsu ya rasu shekara biyu da suka wuce. ‘Yar’uwar Fatima, Anisha Saidu, wadda ke zaune a Unguwar Kofar Ran ta bayyana cewa; ta rasu ne sa’o’i kadan bayan ta fara nuna alamun cutar ta kwalara.

Kwalara
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
Kwalara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
  • Sulaiman
    Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

MASU ALAKA

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft
Labarai

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft
Labarai

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Next Post
Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.