• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daure Wani Mutum Shekara Bakwai Bisa Laifin Lalata Yarinya ‘Yar Shekara 11

byRabi'u Ali Indabawa
12 months ago
Daure

Mai shari’a S. M. Shu’aibu na Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, ya yanke wa wani matashi mai suna Nasiru Isa dan shekara 33 hukuncin daurin shekaru bakwai a gidan yari bisa samunsa da laifin lalata da wata yarinya ‘yar shekara 11.

Wani mai suna Isa, mazaunin Darmanawa Bayan Gidan Kallo a Karamar Hukumar Tarauni ta jihar, an yanke masa hukumcin aikata laifin lalata.

  • Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha
  • Gudunmawar Da Sin Take Bayarwa Wajen Tabbatar Da Wadatar Abinci A Duniya

Alakalin kotun ya ce masu gabatar da kara sun tabbatar wa da mai shari’ar ba tare da wata shakka ba, sannan kotun ta yanke wa wanda ake kara hukuncin daurin shekaru bakwai ba tare da zabin biyan tara ba.

Mai shari’a Shu’aibu ya kuma umurci mai laifin da ya biya tarar Naira miliyan 1 a matsayin diyya.

Tun da farko, hukumar hana fataucin mutane ta kasa reshen Jihar Kano, ta ce Isa ya aikata laifin ne a Unguwar Darmanawa, Karamar Hukumar Tarauni, Jihar Kano a ranar 5 ga Oktoba, 2024.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Lauyan da ya shigar da kara, Abdullahi Babale, ya ce Isa ya yaudari ‘yar makocinsa ‘yar shekara 11 ta hanyar jan ta dakin matarsa inda a nan ne ya yi lalata da ita.

“Isa ya yi lalata da yarinyar a wurare uku.

“Na daya a dakin matarsa sannan kuma biyun a wani gini da ba a kammala ba.

“Wanda aka yanke wa hukuncin ya yaudari yarinyar ne da biredi, gyada da kuma Naira 20 kafin ya yi lalata da ita,” Babale ya shaida wa kotu.

Masu gabatar da kara sun gabatar da abubuwa guda biyu, da suka hada da bayanin ikirari na wanda aka yankewa hukuncin da kuma shaidar wacce aka yi wa ta’asar, ga kotun don tabbatar da gaskiyar lamarin.

A cewar Babale, laifin da aka aikata ya ci karo da sashe na 16 (1) na dokar hana fataucin mutane (Haramci) da tilastawa mutane, ta 2015 kuma laifin yana da hukunci a karkashin sashe na 26 (1) na TIP ACT 2015.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Sin Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Da Wasu Kasashe Suka Yi Wa Manufofinta Na Nukiliya

Sin Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Da Wasu Kasashe Suka Yi Wa Manufofinta Na Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version