• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daure Wani Mutum Shekara Bakwai Bisa Laifin Lalata Yarinya ‘Yar Shekara 11

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Matar Aure Ta Bukaci Kotu Ta Raba Aurenta Da Mijinta Saboda Yawan Jima’i
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai shari’a S. M. Shu’aibu na Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, ya yanke wa wani matashi mai suna Nasiru Isa dan shekara 33 hukuncin daurin shekaru bakwai a gidan yari bisa samunsa da laifin lalata da wata yarinya ‘yar shekara 11.

Wani mai suna Isa, mazaunin Darmanawa Bayan Gidan Kallo a Karamar Hukumar Tarauni ta jihar, an yanke masa hukumcin aikata laifin lalata.

  • Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha
  • Gudunmawar Da Sin Take Bayarwa Wajen Tabbatar Da Wadatar Abinci A Duniya

Alakalin kotun ya ce masu gabatar da kara sun tabbatar wa da mai shari’ar ba tare da wata shakka ba, sannan kotun ta yanke wa wanda ake kara hukuncin daurin shekaru bakwai ba tare da zabin biyan tara ba.

Mai shari’a Shu’aibu ya kuma umurci mai laifin da ya biya tarar Naira miliyan 1 a matsayin diyya.

Tun da farko, hukumar hana fataucin mutane ta kasa reshen Jihar Kano, ta ce Isa ya aikata laifin ne a Unguwar Darmanawa, Karamar Hukumar Tarauni, Jihar Kano a ranar 5 ga Oktoba, 2024.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Lauyan da ya shigar da kara, Abdullahi Babale, ya ce Isa ya yaudari ‘yar makocinsa ‘yar shekara 11 ta hanyar jan ta dakin matarsa inda a nan ne ya yi lalata da ita.

“Isa ya yi lalata da yarinyar a wurare uku.

“Na daya a dakin matarsa sannan kuma biyun a wani gini da ba a kammala ba.

“Wanda aka yanke wa hukuncin ya yaudari yarinyar ne da biredi, gyada da kuma Naira 20 kafin ya yi lalata da ita,” Babale ya shaida wa kotu.

Masu gabatar da kara sun gabatar da abubuwa guda biyu, da suka hada da bayanin ikirari na wanda aka yankewa hukuncin da kuma shaidar wacce aka yi wa ta’asar, ga kotun don tabbatar da gaskiyar lamarin.

A cewar Babale, laifin da aka aikata ya ci karo da sashe na 16 (1) na dokar hana fataucin mutane (Haramci) da tilastawa mutane, ta 2015 kuma laifin yana da hukunci a karkashin sashe na 26 (1) na TIP ACT 2015.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HukunciKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kebbi Ta Kafa Kwamitin Kwato Kuɗaɗen Da Aka Sace A Asusun Marayun Jihar

Next Post

Sin Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Da Wasu Kasashe Suka Yi Wa Manufofinta Na Nukiliya

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

8 hours ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

1 month ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

1 month ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

3 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

4 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

4 months ago
Next Post
Sin Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Da Wasu Kasashe Suka Yi Wa Manufofinta Na Nukiliya

Sin Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Da Wasu Kasashe Suka Yi Wa Manufofinta Na Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.