• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mai Keta Hakkin Bil Adam Na Ikirarin Kare Shi

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Mai Keta Hakkin Bil Adam Na Ikirarin Kare Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan baya, kwamiti na 3 na babban taron MDD karo na 79, ya kira taron muhawara a hedkwatarsa, inda Amurka, da Austriliya da dai wasu kasashe ‘yan tsiraru suka soki kasar Sin kan batun hakkin Bil Adama ba gaira ba dalili.

 

Shin ko wane ne yake da ikon bayyana halin da ake ciki game da wannan batu? Ba shakka jama’a ne da kan su. Sinawa da yawansu ya kai biliyan 1.4 sun fita daga kangin talauci, har ma sun samu wadata tare, suna more rayuwarsu, suna zama cikin kwanciyar hankali, wannan shi ne hakikanin ci gaba a fannin kare hakkin Bil Adam.

  • Musabbabin Lalacewar Lantarki A Jihohin Arewa -TCN
  • Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna…

A wani bangaren na daban, bari mu duba Amurka da Austriliya. Amurka ta dade tana fama da matsalar nuna bambancin launin fata, kana yawan mutanen da suka mutu sakamakon harin bindiga a kasar ya kai kimanin dubu 43 a shekarar 2023 kadai. A sa’i daya kuma, a kalla mutane 1,247 sun mutu a kasar, sakamakon nuna karfin tuwo da ‘yan sanda suke yi. A Austriliya fa? kowa ya san cewa kasar ta samu ci gabanta ne ta hanyar cin zarafin mutane ‘yan asalin wurin da aka kafa kasar.

 

Labarai Masu Nasaba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Wadannan kasashe ba su kula da rayuka, da zaman rayuwar jama’arsu ba, balle na al’ummun sauran kasashe. Yanzu haka, a zirin Gaza, fararen hula fiye da dubu 40 sun mutu, miliyoyin mata da kananan yara na fama da yunwa da rashin muhallin zama. Ba shakka, wannan wuri na matukar bukatar kare hakkin al’ummun sa. Amma, jami’i mai kula da harkokin jin kai a zirin Gaza na kasar Amurka, ya yi ikirarin cewa, gwamnatin Amurka ba za ta daina samarwa Isra’ila makamai ba, duk da cewa matakan da ta dauka a Gaza sun sabawa dokar kasa da kasa.

 

Marigayi masani Publius Cornelius Tacitus, wanda ya mutu a shekaru 2000 da suka gabata, ya taba bayyana cewa, “An nunawa mutane baraguzan gine-gine sun ce wannan shi ne zaman lafiya”, yanzu wasu kasashen yamma suna kokarin ta da rikici a wasu wurare, inda mutane ke fama da asarar rayuka da dimbin wahalhalu, amma sun mai da kansu masu koyar da mutanen duniya dabarar kare hakkin Bil Adam, gami da shafawa kasar Sin bakin fenti, duk da iyakacin kokarin da kasar ke yi a fannin kare hakkin da ikon jama’arta.

 

Sai dai wadannan kasashen ba za su iya mai da fari baki ba. Ko da yake sun dade suna kokarin dora laifi kan kasar Sin, kan batun hakkin Bil Adam, amma yawancin kasashe ba su taba yarda da maganarsu ba.

 

Tabbas, zamani na yin shisshigi cikin harkokin gidan sauran kasashe bisa hujjar kare hakkin Bil Adama ya kai karshensa. (Mai zane da rubutu: MINA)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi, Ya Yi Karin Haske Game Da Halartar Taron BRICS Karo 16 Da Shugaba Xi Ya Yi

Next Post

Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

Related

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

4 days ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

1 week ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

1 week ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

1 week ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

1 week ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

2 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.