• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ‘Yan Siyasar Arewa Sun Shiga Rudani Wajen Lalubo Dan Takarar Da Zai Kalubalanci Tinubu

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahotanni sun bayyana cewa wasu shugabannin siyasa a yankin arewa sun shiga rudani wajen lalubo dan takarar da za su mara wa baya a zaben shugaban kasa mai zuwa, domin kalubalantar Shugaban kasa Bola Tinubu.

An bayyana cewa wasu daga cikin shugabannin arewa ba su gamsu da halin da al’ummar kasar ke ciki ba, wanda a tunaninsu lamarin ya fi tasiri a yankin arewa. Rahotanni sun nuna cewa shugabannin siyasan a arewa sun ce gwamnatin Shugaba Tinubu ta yi watsi da su, duk da goyon bayan da suka bayar a zaben da ya gabata, suna masu ikirarin cewa arewa ba ta ci gajiyar abin da ake tsammani ba.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • EU Za Ta Janyowa Kan Ta Lahani Sakamakon Kakaba Karin Haraji Kan Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin

Duk da cewa zaben 2027 ya rage saura ‘yan shekaru kadan, amma an bayyana cewa dattawan arewa na kara zage dantse wajen lalubo zaratan ‘yan takara masu nagarta don kalubalantar shugabanni masu ci a yanzu. Wasu fitattun ‘yan siyasa a yankin arewa maso yamma sun yi taro wajen tattaunawa kan dan takarar da zai iya doke Shugaba Tinubu a zaben 2027.

Haka kuma wasu masu taimaka wa gwamnonin arewa sun tabbatar da wannan tattaunawa, inda suka yi nuni da cewa, zaben 2027 ne ke gaban manyan ’yan siyasar arewa da suka hada da shugabanninsu. Rahotanni sun bayyana cewa wadannan ‘yan siyasan na auna hadarin da ke tattare da adawa da Shugaba Tinubu bayan ya samu nasara a zaben 2023.

Wani kalubalen da ke gaban shugabannin arewa shi ne, zaben dan takarar da zai samu karbuwa sosai a arewa tare da yin la’akari da dabarun adawa, kamar jaddada tsarin shiyya-shiyya da muradun Kudu.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

“Su shugabannin arewa sun yi imanin cewa hanya mafi dacewa ita ce a goyi bayan fitaccen dan siyasar kudu,” in ji wata majiya, “amma duk da haka sun damu wajen lalubo wani daga kudu da zai dace da Shugaba Tinubu a matsayinsa da kuma karfin kudi.”

Duk da cewa ba a yanke hukunci a hukumance ba, majiyoyi sun ce an fara fitar da jerin sunayen ‘yan takara da kuma mataimakansu

“Watakila za a zabi wani sahihanci dan siyasa daga yankin arewa maso yamma a matsayin abokin takara,” in ji wata majiya mai tushe, inda ta bayyana cewa Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso, tsohon gwamnan Jihar Kano, da Alhaji Aminu Tambuwal suna cikin sunayen da aka zayyana.

“A halin yanzu, ‘yan siyasar arewa na ci gaba da neman wanda zai iya tsayawa takara a 2027. Duk da haka, zai yi wuya su sake mara wa wannan gwamnati baya,” in ji majiyar, lamarin da ke nuni da cewa har yanzu siyasar arewa ta yi nisa.

Bugu da kari kan nuna damuwa da yadda wannan gwamnati ke kara samun rashin inganci, rahotanni sun nuna cewa shugabannin arewa sun yi taka-tsan-tsan game da koma bayan da ‘yan mazabarsu za su iya fuskanta idan suka ci gaba da mara wa Shugaba Tinubu baya a 2027.

Kasancewar rashin aikin yi da hauhawar farashin kayayyaki da rashin tsaro da ke addabar al’ummar arewa, shugabannin na fargabar cewa amincewa da shugabancin da ba a canza ba zai iya raba kan matasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewatakaraTinubuZaben 2027
ShareTweetSendShare
Previous Post

Man Utd Ta Dauki Ruben Amorim A Matsayin Sabon Kocinta

Next Post

MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

Related

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

6 days ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

6 days ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

4 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

4 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

4 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

1 month ago
Next Post
MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.