• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
in Manyan Labarai
0
Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rikicin cikin gida da ke gudana cikin jam’iyyar NNPP mai mulki a Jihar Kano ya ƙara ta’azzara yayin da ake zargin Gwamna Abba Yusuf ya daina ɗaukar kiran jagoransa, Rabiu Kwankwaso, abin da ya haifar da kiraye-kirayen da ke nuna cewa lokaci ya yi da gwamnan zai nemi ‘yancin kansa daga Kwankwaso.

Kalmar “Abba Tsaya da Kafarka” ta zama ruwan dare, yayin da magoya baya ke kira ga gwamnan ya kame kansa.

  • Gwamna Abba Ya Amince Da Sabon Mafi Karancin Albashi Na ₦71,000 Ga Ma’aikatan Kano
  • Ƙungiyar Likitoci Ta Buƙaci Dakatar Da Kwamishina Kan Zargin Cin Zarafin Likita A Kano

Wannan rikici ya fara tsananta ne bayan wasu membobin NNPP sun sami umarnin kotu da ke ba su damar mallakar ikon jagorancin jam’iyyar ga tsohon shugaban jam’iyyar Boniface Aniebonam, wanda hakan ya rage tasirin Kwankwaso.

Gwamna Yusuf, wanda ke nuna rashin jin daɗi kan tsoma bakin Kwankwaso, musamman a naɗe-naɗen ƙananan hukumomi, ya kori shugabannin riƙon ƙwarya na ƙananan hukumomi, da sabanin umarnin Kwankwaso na tsawaita wa’adinsu.

Wannan rashin jituwa ta sake bayyana a ranar 21 ga Oktoba, lokacin da suka haɗu a wajen bikin murnar zagayowar ranar haihuwa, amma tun daga nan ba su sake yin magana sosai ba.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Masu goyon bayan gwamnan sun nesanta kansu daga ƙungiyar Kwankwasiyya, wanda Kwankwaso ya kafa, yayin da kiraye-kiraye ke ƙaruwa don Gwamna Yusuf ya nuna cikakken ikon kansa. Yayin da wasu ‘ya’yan NNPP ke ƙara juya baya ga Kwankwaso, magoya bayansa sun yi tir da gwamnan bisa abin da suka kira rashin biyayya.

Amma har yanzu ba a samu bayani daga bangarorin biyun ba kan lamarin.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba KabirYusufkanoKwankwasiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista

Next Post

Firaministan Sin Ya Jaddada Bukatar Karfafa Ilimin Sana’o’in Hannu Da Samar Da Kwararrun Ma’aikata

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

9 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

14 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

15 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

23 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

1 day ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
Firaministan Sin Ya Jaddada Bukatar Karfafa Ilimin Sana’o’in Hannu Da Samar Da Kwararrun Ma’aikata

Firaministan Sin Ya Jaddada Bukatar Karfafa Ilimin Sana’o’in Hannu Da Samar Da Kwararrun Ma’aikata

LABARAI MASU NASABA

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Gwamna

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.