• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO

by Sulaiman and Abubakar Abba
9 months ago
in Noma Da Kiwo
0
‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar samar da abinci da kula da aikin noma ta duniya (FAO), ta sanar da cewa; a halin yanzu ‘yan Nijeriya miliyan 1.8 ne ke fama da matsalar yunwa.

Karamin Ministan Ma’aikatar Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Aliyu Sabi Abdullahi; ya sanar da hakan ne a Abuja, wajen taron manema labarai.

  • MDD Za Ta Yi Duk Mai Yiwuwa Wajen Taimaka Wa Nijeriya Kawo Karshen Talauci
  • Kamfanoni 80 Sun Bayyana Burinsu Na Halartar Baje Kolin CIIE Karo Na 8

Sai dai, Abdullahi ya shelanta cewa; gwamnatin tarayya ta mayar da hankali wajen yakar rashin abinci a kasar, inda ya yi nuni da cewa; a 2023, mutane miliyan 733 ne ke fuskantar yunwa a dukkanin fadin duniya.

Ministan, wanda ya bayyana haka a bikin ranar abinci ta duniya da aka gudanar a kwanakin baya ya ci gaba da cewa, bisa rahoton yanzu da hukumar FAO ta wallafa kan karancin abinci da kuma abinci mara gina jiki da mutane ke fuskanta ya kai miliyan 733 a 2023 a fadin duniya.

Ya kara da cewa, kimanin mutane biliyan 2.33 sun fuskanci karancin abinci a 2023, inda kuma mutane biliyan 2.8 a 2022, ba sa iya samun abinci mai gina jiki.

Labarai Masu Nasaba

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Ya yi gargadin cewa, idan har mahukunta a kasar ba su dauki matakan da suka kamata ba, kimanin ‘yan Nijeriya miliyan 582 ne za su fuskanci rashin samun abinci mai gina jiki nan da 2030.

Abdullahi ya sanar da cewa, akwai manyan kalubale da dama da suka haifar da karancin abinci a duniya da suka hada da sauyin yanayi, fari, yawan samun ruwan sama da sauransu.

A cewar tasa, wadannan kalubalen sun kasance barazana a kan harkokin noma baki-daya, sannan kuma ya danganta da karancin abincin da ake ci gaba da samu a kasar sakamakon rashin tsaro, matsin tattalin arziki, annobar ambaliyar ruwan sama da kuma cire tallafin mai.

Sai dai, ya sanar da cewa; don mangance wadannan kalubale, wadanda kuma suka zamo karfen kafa wajen cimma burin da gwamnatin tarayya ta sanya a gaba na samar da wadataccen abinci a kasar, gwamnatin ta wanzar da sauye-sauye da dama da suka hada da kirkiro da ayyukan yi da kuma rage tsadar kayan abinci.

Ya kara da cewa, dole ne har sai masu ruwa da tsaki a wannan kasa, su ma sun bayar da tasu gudunmawar; kafin a iya kawo karshen wadannan matsaloli.

A cewarsa, a shekarar 2017; Nijeriya ta samu gagarumar nasara a fannin aikin noma a duniya, inda ta kai mataki na daya a fannin noman Rogo da Doya, inda ta noma wadannan amfani da suka kai kimanin tan miliyan 59.4 da kuma tan miliyan 47.9 baki-daya.

Bugu da kari, ya kara da cewa; Nijeriya ta kai mataki na 14 wajen noman Masara, inda ta noma tan miliyan 10.42; ta kai mataki na hudu a fannin noman Kwakwar manja, inda ta noma tan miliyan 7.7 a cikin shekara guda.
Kazalika a 2019, Nijeriya ce kan gaba wajen noman Shinkafa a dukkanin Nahiyar Afirka, inda aka noma tan miliyan tara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kangin TalauciYunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kingibe Ya Yaba Wa Tsare-tsaren Bunkasa Ilimi Ga Matasa Na Buratai

Next Post

Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

Related

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

1 day ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

2 days ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

1 week ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

1 week ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Next Post
Discos

Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.