ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Da EU Sun Kulla Yarjejeniyar Bunkasa Wutar Lantarki

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
Discos

Gwamnatin Tarayya ta rattaba hannun yarjejeniya da kungiyar tarayyar turayyar turai wato EU, da kuma gwamnatin kasar Jamus.

Sun kulla yarjejeniyar ce, domin a zuba Fam miliyan 17.9 a aikin babban layin wutar lantarki na kasar nan.

  • ‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ne Ke Fama Da Matsalar Yunwa – Hukumar FAO
  • Harajin “VAT” Zai Kara Wa Al’ummar Kasar Nan Kuncin Rayuwa Ne Kawai – Gambo Danpass

An kaddamar da aikin ne, a karkashin shiri kashi na uku, na tallafwa fannin makamashi tare da samar da haske da kuma samar da wutar lantaki a karkara.

ADVERTISEMENT

Shirin na EU, zai bai wa jama’a 154,000 samun wutar da kuma hada sauran mutane 30,000 domin su samu iskar Gas.

Kazalika, a kashi na uku, za a kuma samar da megawatt ta wuta guda takwas.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

A 2013 ne, aka kaddamar da shirin wanda EU da ma’aikatar bunkasa tattalin arziki ta kasar Jamus, tare da hadaka da Deutsche Gesellschaft für Internationale Zusammenarbeit da ma’a’ikatar kula da makamsshi, domin ya taimakawa Nijeriya
A jawabinta a wajen kaddamarwar da a wata ganawa dangane da shirin na NESP kashi na uku, shugabar sashen bunkasa tattalin arziki ta fasahar zamani a EU Inga Stefanowicz, ta yi nuni da cewa, domin a cimma burin yin kasuwanci na sahishi, aiki ne da ya rayata a kan kowanne mai ruwa da tsaki a fannin.

Inga wadda kuma ita ce ta jagoranci tawagar zuwa Nijeriya da zuwa kungiyar ECOWAS ta ce, EU ta jima ta na taimakawa Nijeriya domin ta cimma burinta na samar da tsaro a fannin samar da makamashi.

Ta kara da cewa, EU ta kuma taimakawa Nijeriya, a kan cimma burinta na ci gaba da wanzar da fannin makamashin ta, musamman wajen kara gwama yawan makamashin ta a fannin samar da wutar lantarki.

Ta ci gaba da cewa, a yayin da aka kadfdamar da wannan kashin na uku, a nan gaba za a kuma kaddamar da wasu, wanda ta ce, a wannan sabon shirin mutane 154,000 za su samu wutar lanrkin, inda kuma mutane 30,000, za su samu ingantacciyar iskar Gas na yin girgi na LPG.

Ta ce, akwai kuma tsarin kara samar da karin megawatt takwas ta makamashi tare da kafa hasken wuta na sola a cikin aikin kiwon lafiya.

Shi ma a na sa jawabin a wajen kaddamarwar mataimakin Jakadan kasar Jamsu Johannes Lehne, ya nanata kudurin gwamnatin Jamus na ci gaba da taimakawa Nijeriya, domin ta cimma burinta na aikin samar da makashi.

Ya bayyana cewa, shirin kashi na uku, ma’aikatar bunkasa tattalin arziki ta kasar Jamsu ce, ta kaddamar dashi awatan Mayun 2024, inda ta zuba Fam miliyan 8.9.

Ya kara da cewa, tun a baya, EU hukumar ta kuma kaddamar karin wata Fam miliyan 9, wanda hakan ya kara kasafin jaimmlar shirin, zuwa Fam miliyan 17.9.

Shi kuwa a na sa jawabin a wajen kaddamawar babban sakatare a ma’aikatar samar da wutar lantarki Mahmuda Mamman ya bayyana cewa, aikin zai taimaka, musamman domin a ciki gibin ‘yan Nijeriya miliyan 100, da har yanzu, ba su iya samun wutar lantarki.

Ya sanar da cewa, yin amfanin da makamashin zai rage kalubalen da aka fuskanta na rashin samun wutar lantarki a kasar, musamman a karkara.

Ya bayyana cewa, shirin kashi na uku, ya samu nasara ne, saboda yadda aka samu nasara a kashi na daya da kuma na biyu, na shirin.

A cewarsa, a kashi na daya da na biyun, an kara yawan wutar da ake turawa zuwa ga alumomin da ke a karkara.

Shi kuwa shugaban shirin na NESP, Duke Benjamin, ya bayyana cewa, an faro aikin ne a shekarar 2013, wanda kuma zai samar da wutar lantarki zuwa ga alumomin da ke zaune a karkara, idan aka sanya su a babban layin samar da wautar lantarki na k

Wutar Lantarki
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Wutar Lantarki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ba Za Ta Samu Wani Sabon Bashi Daga Bankin AfDB Ba -Farfesa Oyebanji

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ba Za Ta Samu Wani Sabon Bashi Daga Bankin AfDB Ba -Farfesa Oyebanji

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.