• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Sasanta Batun Nukiliyar Iran A Siyasance

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Sasanta Batun Nukiliyar Iran A Siyasance
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wakilin kasar Sin ya bayyana cewa, arangama ba zai iya warware batun nukiliyar kasar Iran ba, yana mai kira da a warware batun ta hanyar siyasa da diflomasiyya. 

 

Zaunannen wakilin kasar Sin a hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA Li Song ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin da kwamitin gwamnonin kasashe 35 na hukumar suka zartas da wani kuduri da ke matsawa Iran lamba kan nukiliyarta.

  • Makarantu Masu Zaman Kansu Sun Koka Kan Kudaden Tafiyar Da Ayyukansu
  • Farfesa Zaynab Alkali: Mace Ta Farko Da Ta Zama Marubuciyar Littattafai Daga Arewacin Nijeriya

Kasashen Sin da Rasha da Burkina faso sun kada kuri’ar kin amincewa da kudurin da Amurka da Birtaniya da Faransa da kuma Jamus suka gabatar, yayin da kasashe 12 masu tasowa da suka hada da Afirka ta Kudu da Indiya da Masar suka kaurace.

 

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

Li ya kara da cewa: “Hakikanan gaskiya sun tabbatar da cewa, kirkiro sabani tsakanin juna, da kara tashe-tashen hankula a cikin kwamitin ba zai warware matsalar ba, sai dai zai iya haifar da tabarbarewar hadin gwiwa tsakanin hukumar da Iran, da kuma kara dagula lamarin,” yana mai jaddada cewa, matsa lamba ba tsarin diflomasiyya ba ce, kuma adawa ba za ta iya samar da mafita ba.

 

Wakilin na kasar Sin ya bayyana cewa muhimman hanyoyin warware matsalolin da suka shafi dakile matsalar sun ta’allaka ne a kokarin siyasa da diflomasiyya, da kuma yin hadin gwiwa mai ma’ana kan dandalin bangarori daban daban.

 

Li ya kuma bukaci bangarorin da abin ya shafa da su kalli lamarin cikin “tsanaki da sanin ya kamata” tare da taka rawa mai ma’ana wajen warware batun nukiliyar Iran a siyasance. (Mohammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwa 10 Game Da Karin Tsintsiyar Hannu

Next Post

Ƙanin Kwankwaso Ya Maka Gwamnan Kano A Kotu Kan Batun Fili

Related

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

19 hours ago
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

20 hours ago
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara
Daga Birnin Sin

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

21 hours ago
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

22 hours ago
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

23 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

1 day ago
Next Post
Ƙanin Kwankwaso Ya Maka Gwamnan Kano A Kotu Kan Batun Fili

Ƙanin Kwankwaso Ya Maka Gwamnan Kano A Kotu Kan Batun Fili

LABARAI MASU NASABA

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

September 5, 2025
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

September 5, 2025
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

September 5, 2025
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Kwalaben Akuskura Sama Da 8,000 A Kano

September 5, 2025
'Yan Bindiga

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

September 5, 2025
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

September 5, 2025
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

September 5, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Jimamin Rasuwar Mutane A Nutsewar Jirgin Ruwa A Borgu, Ta Umurci NEMA Ta Kai Agaji 

September 5, 2025
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.