• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi

by Khalid Idris Doya
5 months ago
in Tattalin Arziki
0
Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Wale Edun, ya ce, gwamnatin tarayya tana bukatar karin wasu basukan kudade domin ta cike gibin kasafin kudinta, duk kuwa da cewa wasu ma’aikatu da rassa da sashi-sashi sun inganta harsashen hanyoyin shigar kudinsu.

Ministan ya shaida hakan ne yayin ganawa da hadakar kwamitin majalisar dattawa na kudin da na tsare-tsaren harkokin tattalin arziki kan tsarin kashe kudade na 2025 zuwa 2027.

  • Dikko Radda Ya Bai Wa Gwarazan Hikayata Kyautar Kudi
  • Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a

Edun ya ce akwai bukatar cikin basukan muddin majalisar dattawa ta amince da hakan.

“Yunkurin da ake yi kan kudin shiga yana tafiya daidai, amma akwai bukatar a kara himma, muna bukatar karin basuka masu albarka, inganci da dourewa.

“Ba kawai don gine-gine da manyan ayyukan ba, har ma don ayyukan jin dadi da walwalar jama’a, ayyukan kiwon lafiya, ilimi da ayyuka a fannonin kiyaye tsaron jama’a don taimaka wa masu karamin karfi da masu fama da talauci,” Edun ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

A nasa bangaren, ministan kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki, Sanata Atiku Bagudu ya tunatar da ‘yan majalisar yunkurin ciwo bashi tiriliyan 35.5 a kasafin 2024, da farko an yi nufin sanar da gibin tiriliyan 9.7.

“Duk da tsare-tsaren kudaden shiga ya zarta na wasu hukumomin samar da kudaden shiga, har yanzu akwai bukatar gwamnati ta karbo rancen kudade don gudanar da kasafin kudin yadda ya kamata, musamman ta fuskar rabe-rabe da samar da ayyukan yi ga marasa galihu.

“Muna da tsarin hangen nesa na ci gaba na dogon lokaci na 2050,” in ji Bagudu.

Kazalika, shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC), Ola Olukoyede, ya shaida wa kwamitin cewa hukumarsa ta kwato sama da naira biliyan 197 daga watan Janairun 2024,

Ya lura cewa idan gwamnati ta yi aiki tukuru kuma ta samu tarin abubuwan da ake bukata, kasar za ta samu isassun kudaden da za ta kashe a kasafin kudin.

Babban Kwanturolan Hukumar Kwastam ta Nijeriya, Bashir Adeniyi, a cikin jawabinsa, ya bayyana cewa hukumar ta kwastam ta tara naira tiriliyan 5.352 na kudaden shiga fiye da naira tiriliyan 5.09 da aka yi niyyar yi a kasafin kudin shekarar 2024.

Ya ci gaba da cewa, naira tiriliyan 6.3 an yi niyya ne a matsayin kudaden shiga da aka yi hasashen za a samu a shekarar 2025, wanda kasha 10 daga ciki zai kasance abin da ake sa ran samun kudaden shiga a shekarar 2026 da karin kashi 10 na kasafin kudin shekarar 2027.

A nasa jawabin, babban jami’in gudanarwa na rukunin kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL), Mele Kyari, ya ce kamfanin ya zarce kudaden shiga na naira tiriliyan 12.3 da aka yi hasashen za a iya samu a shekarar 2024, inda ya riga ya tara naira tiriliyan 13.1.

Har ila yau, shugaban hukumar tara haraji ta kasa FIRS, Zacch Adedeji, a nasa jawabin, ya sanar da kwamitocin hadin gwiwa cewa FIRS ta zarce kudaden shiga da aka yi niyya a sassa daban-daban na haraji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Rahoto Ya Fallasa Hanyoyin Da Doka Ta Tanada Don Kare Masu Aikata Fyaɗe A Afirka

Next Post

Kidayar Jama’a Da Harkar Lafiya

Related

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 weeks ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

3 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

3 weeks ago
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

4 weeks ago
Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
Tattalin Arziki

Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

4 weeks ago
Next Post
Kidayar Jama’a Da Harkar Lafiya

Kidayar Jama'a Da Harkar Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.