Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, ya bayyana sanye da kaya na alfarma don shugabantar zaman fada duk da ƙawanyar da jami’an tsaro suka yi wa fadar a yau Jumma’a.
Sarki Sanusi II, tare da sauran ma’aikatan fadar, ya ci gaba da gudanar da zaman fadar cikin natsuwa a fadar. Jami’an ‘Yansanda na Kano ba su bayar da bayanin dalilin ƙawanyar ba, wanda ya ƙara jawo tambayoyi kan lamarin ruɗanin sarauta da ke faruwa a jihar.
- Na Sha Gwagwarmaya Wajen Koyon Ka’idojin Rubutu – Zarah Sunusi
- Kiyaye Rayukan Al’umma: Majalisa Na Shirin Keɓe Wa Masu Sayar Da Iskar Gas Wuri A Wajen Birnin Kano
Haka kuma, babu wani bayani daga majalisar fadar Kano game da taron sarauta da Sarki Sanusi II ya shirya halartar a Bichi.
Rahotanni daga Gidan Gwamnatin jihar sun bayyana cewa gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, yana ƙasar Indiya yin wata ziyara aiki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp