• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za A Bar Kowace Kasa A Baya Ba A Kokarinsu Na Zamanintar Da Kansu

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Ba Za A Bar Kowace Kasa A Baya Ba A Kokarinsu Na Zamanintar Da Kansu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun daga ranar 1 ga wannan watan da muke ciki ne kasar Sin ta soke harajin kwastam a kan dukkanin kayayyakin da take shigowa daga kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba, wadanda suka kulla huldar diplomasiyya da ita a hukumance, ciki har da wasu kasashe 33 dake nahiyar Afirka. Hakan ya sanya ta zama kasa mai tasowa ta farko a duniya da ta dauki irin wannan mataki. A game da hakan, Dennis Munene Mwaniki, darektan zartaswa na sashen kula da harkokin Sin da Afirka karkashin cibiyar nazarin manufofin Afirka da ke kasar Kenya, ya ce, matakin da kasar Sin ta dauka na soke haraji zai taimakawa kasashe masu tasowa na fadin duniya wajen saukaka fatara da kuma gaggauta zamanintar da kansu.

 

Kasancewarta kasa mai tasowa mafi girma a duniya, kasar Sin tana sane da cewa, tabbatar da ci gaba shi ne ainihin matakin da zai taimaka wajen warware dukkanin matsaloli masu nasaba da talauci. Don haka, kasar Sin na ganin cewa, dole ne a tabbatar da bunkasuwar kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba, a maimakon samar musu da taimako kawai.

  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani
  • Kasar Sin Na Mai Da Hankali A Kan Halin Da Ake Ciki A Syria

Lallai, matakin da kasar Sin ta dauka a wannan karo na soke harajin kwastan, ya kasance mataki na tabbatar da bunkasuwar kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba. Sanin kowa ne kasashen ba sa rasa kayayyaki masu inganci, sai dai sun kasa samun damar shiga kasuwannin duniya, wasu kuma sabo da yawan kudin da za su biya don fitar da kayayyakinsu zuwa ketare. Ga shi yanzu, yadda kasar Sin ta soke harajin kwastan ya samar da kyawawan sharudda ga kasashen da matakin ya shafa wajen fitar da kayayyakinsu masu inganci zuwa kasar Sin, kuma hakan tabbas zai sa kaimin bunkasuwar sana’o’in kasashen, tare da sa kaimi ga samar da guraben aikin yi da saukaka fatara. Muna iya hasashen cewa, bisa ga matakin, kayayyaki masu inganci na kasashen da suka fi fama da rashin ci gaba a Afirka, ciki har da abarba na Benin da gahawa na Habasha da tattasai na Rwanda da zuma na Tanzania, sai kuma naman rago na Madagarscar, za su gaggauta shiga babbar kasuwar kasar Sin, wanda hakan zai samar musu babbar damar tabbatar da ci gabansu.

 

Labarai Masu Nasaba

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Zamanintar da kansu buri daya ne ga Sin da kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa. A lokacin da take kokarin zamanintar da kanta, kasar Sin ba ta son ganin ita kadai ta cimma burinta, a maimakon haka, tana son ganin kowa burinsa ya cika. Don haka, a lokacin da take raya kanta, har kullum kasar Sin na dukufa a kan raba damammakinta ga kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa. Hakika, ban da matakin nan na soke harajin kwastan, ta kuma samar da kafar musamman ga kayayyakin amfanin gona da kasashen Afirka ke fitarwa zuwa gare ta, tare da samar da sauki ga kamfanonin kasashen Afirka wajen halartar bukukuwan baje kolin da ta shirya, irinsu bikin baje kolin kayayyaki da suke shigowa daga ketare, baya ga haka, ta kuma samar musu taimako wajen horar da kwararru, da dai sauransu.

 

A gun taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen Afirka da aka gudanar a watan Satumban bana a birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabin cewa, ba za a bar kowace kasa a baya ba a kokarin da suke yi na zamanintar da kansu. Dukkanin kasashen Sin da Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa, sai mu hada karfi da karfe, domin cimma wannan burinmu na bai daya. (Lubabatu)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani

Next Post

Dokar Haraji: Ƙarawa Masu Kudi Haraji Ba Talakawa Ba Shi Ya Kamata

Related

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

19 hours ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

3 days ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

1 week ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

1 week ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

1 week ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Next Post
Dokar Haraji: Ƙarawa Masu Kudi Haraji Ba Talakawa Ba Shi Ya Kamata

Dokar Haraji: Ƙarawa Masu Kudi Haraji Ba Talakawa Ba Shi Ya Kamata

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 16/05/2025

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

June 27, 2025
Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

June 27, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.