ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Sin

A gun taron ministoci game da tantance ayyukan aiwatar da sakamakon da aka samu a dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, da ya gudana a birnin Changsha na Sin a kwanan nan, kasar Sin ta sanar da cewa, za ta yafe harajin fito kan dukkan kayayyakin kasashe 53 dake nahiyar Afirka da ta kulla huldar diplomasiyya da su. Hakan ya nuna cewa, kasar Sin tana kokarin cika alkawarin da ta yi na gina “al’ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makomar bai daya”.

Ban da kasashe 33 masu karancin tattalin arziki dake nahiyar Afirka, da tuni suka ci gajiyar manufar Sin ta yafe harajin kwastam, sabbin kasashe 20 dake Afirka da za su ci gajiyar manufar, sun hada da Najeriya, da Masar, da Afirka ta Kudu, da kuma Aljeriya, wato kasashe hudu mafi karfin tattalin arziki a Afirka. Wadannan kasashe, a bisa tushen karfinsu a fannin tattalin arziki, za su iya amfani da manufar kasar Sin wajen kara habaka bangaren fitar da kayayyaki zuwa kasuwannin Sin sosai. Bugu da kari, game da wasu kasashen Afirka da ke da gibin ciniki da kasar Sin, manufar yafe haraji ta kasar za ta taimaka wajen daidaita cinikayyarsu da kasar Sin.

  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna

Idan aka waiwayi yadda aka raya dangantakar tattalin arziki da ciniki tsakanin Sin da Afirka cikin shekaru 20 da suka gabata, za mu iya ganin cewa, manufar rangwame a fannin harajin kwastam da kasar Sin ta samar wa kasashen Afirka ta yi ta fadada zuwa fannoni daban daban.

ADVERTISEMENT

Tun a shekarar 2005, kasar Sin ta fara daukar matakan rage harajin fito kan kayayyakin kasashen Afirka da ke da raunin tattalin arziki, kuma ya zuwa shekarar 2010, manufar ta shafi kashi 60 cikin 100 na kayayyakin kasashe 26 dake nahiyar Afirka. Sa’an nan, daga shekarar 2022, kasar Sin sannu a hankali ta fara aiwatar da matakin yafe haraji kan kaso 98% na kayayyakin kasashe 27 dake Afirka. Bayan haka, a gun taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na shekarar 2024 da aka gudanar a birnin Beijing, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya sanar da yafe harajin kwastam kan dukkan kayayyakin da ake shigowa kasar Sin daga kasashen Afirka 33 da suka fi fama da koma bayan tattalin arziki wadanda suka kulla huldar diplomasiyya tare da ita. Sai kuma ga shi a yanzu, manufar yafe haraji ta kasar Sin ta shafi dukkan kasashe 53 dake nahiyar Afirka, da suka kulla huldar diplomasiyya tare da ita.

Ba kamar wasu matakan ciniki da suka jibanci Afirka, da kasashen yamma suka gabatar a baya ba, wadanda ke shafar manufofin siyasa da yunkurin gyaran tsare-tsaren Afirka, manufofin kasar Sin suna da halayen musamman guda uku: Wato da farko, ba a taba gindaya sharadi na siyasa ba. Kana na biyu, manufofin suna dorewa. Gami da na uku, wato kasar na tare da burin tabbatar da ci gaban tattalin arzikin Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

Ta hanyar inganta manufar yafe harajin kwastam a kai a kai, kasar Sin ta samar da yanayin kasuwanci mai karko a kasashen Afirka. Bugu da kari, kasar Sin tana kallon manufofinta na rangwame a matsayin matakan tabbatar da burin samun ci gaba, inda take kokarin kyautata tsarin cinikayyar waje na kasashen Afirka, da kuma ba da goyon baya wajen raya masana’antu, da habaka tsare-tsaren tattalin arziki a Afirka.

Dalilin da ya sa kasar Sin ke kokarin tabbatar da ci gabanta da kasashen Afirka na bai daya, shi ne domin ra’ayinta game da dangantakar dake tsakaninta da Afirka, wato al’ummar Sin da Afirka suna da makomar bai daya a nan gaba. A ganin kasar Sin, ita da Afirka suna da tarihi masu kama da juna, da kuma bukatun bai daya na raya kasa. Sa’an nan, a zamanin da muke ciki, yayin da ake fuskantar sauye-sauye a fannonin siyasa, da tattalin arziki, da kimiyya da fasaha, kasashe masu tasowa na cikin wani yanayi mai wuya ta fuskar raya tattalin arzikinsu. Saboda haka, Sin da Afirka ba za su iya cimma burinsu na samun ci gaban bai daya ba, sai dai ta hanyar hadin gwiwa da juna, a bangarorin tabbatar da adalci da gaskiya a duniya , da bude kofa, da tabbatar da moriyar kowa, da kyautata muhalli, da kuma kiyaye zaman lafiya. Bisa kokarin da ake na sauya nagartaccen tunani zuwa hakikanan matakai, ko shakka babu za mu shaida karin nasarorin da Sin da Afirka za su samu, a kokarinsu na zamanantar da al’ummunsu tare. (Bello Wang)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

MASU ALAKA

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya
Ra'ayi Riga

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Next Post
Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne - Obasanjo

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.