• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya yi garambawul a gwamnatinsa, sannan ya rantsar da wani sabon Kwamishina.

 

A Litinin ɗin nan ne Gwamna Dauda Lawal ya jagoranci zaman majalisar zartarwar jihar, inda a lokacin zaman ya rantsar da wani sabon Kwamishina.

  • Kamfanin Turkiyya Ya Fara Aikin inganta Noman Zamani A Zamfara 
  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani

A cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa a wannan zaman Majalisar, gwamnan ya canja wa wasu Kwamishinoni wuraren aiki.

Sanarwar ta ce, an naɗa sabon Kwamishinan, Kasimu Sani Kaura ne don ya maye girbin Mannir Muazu Haidara, wanda ya ajiye aiki, kuma aka zaɓe shi a matsayin Shugaban Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Gwamna Lawal ya bayyana wa Majalisar cewa dacewa ce ta sa aka zaɓo Kasimu Sani Kaura don ya wakilci al’ummar Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda a Majalisar, wanda kuma ya kasance mutum ne jajirtacce game da ci gaban al’ummarsa, da ma jihar baki ɗaya.

Gwamnan ya ce, “Wannan naɗi, wata alamar tabbaci ce ta gwamnatin nan na zaƙulo jajirtattun mutanen da za su bayar da gagarumar gudumawa wajen inganta rayuwar al’umma da ci gaban jihar Zamfara.

“Ina mai yin kira ga sabon Kwamishinan kan ya bayar da rayuwarsa wajen yi wa al’ummar sa hidima. A matsayin sa na mamba a harkar ceto jihar Zamfara, ba ni da shakkun irin gagarumar gudumawar da zai bayar don amfanin jama’a.

“Mai girma Kwamishina, ina taya ka murnar wannan kira da aka yi maka don ka yi wa al’umma hidama. Ina maka, tare da dukkan mu fatan tsarewar Allah. Ina mai kira gare ka da ka kasance kana aiki kafaɗa da kafaɗa tare da sauran Kwamishinoni, da kuma ma’aikatan ma’aikatarka.

Gwamnan ya ce, ya lura da yadda dukkan muƙarrabansa ke gudanar da ayyukansu, wanda hakan ne ta sa ya yi wasu ‘yan canje-canje. “Don ganin mun samu nasarar sauke nauyin da ke kanmu, ina ganin akwai buƙatuwar yin wasu ‘yan canje-canje a gwamnatina.”

“Wannan sabon Kwamishina, Kasimu Sani Kaura, zai kula da ma’aikatar muhalli da albarkatun ƙasa, inda ya maye gurbin Hon. Mahmud Mohammed Abdullahi, Wanda aka mayar da shi mai kula da ma’aikatar yaɗa labarai da al’adu.

“Hon. Nasiru Ibrahim Zurmi kuma ya koma Kwamishina a ma’aikatar kula da birane, inda ya maye gurbin Hon. Kabiru Moyi, wanda ya koma. Ma’aikatar sanya ido da aiwatar da ayyuka.

“Bugu da ƙari, an canja Dr. Nafisa Muhammad zuwa ma’aikatar lafiya, inda ta maye gurbin Dr. Aisha M. Za Anka, wacce ta koma Kwamishina a ma’aikatar kula da mata da inganta jin daɗin jama’a.

“Za a kammala duk wasu shirye-shiryen miƙa shugabancin a tsakanin kwanaki bakwai. Ina so in ƙara tunatar da ku cewa zan ci gaba da sanya ido da yadda kuke gudanarwa, tare da auna ayyukanku, domin muna fuskantar rabin wa’adinmu a ofis. Mu yi amfani da wannan dama wajen jajircewa da sadaukarwa wajen yi wa jihar mu ta Zamfara hidima.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LakurawaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Inuwar Gamji

Next Post

Jagororin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Sun Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki Da Ayyukan Jam’iyya Da Yaki Da Cin Hanci Na 2025

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

1 hour ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

4 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

5 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

14 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

16 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

17 hours ago
Next Post
Jagororin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Sun Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki Da Ayyukan Jam’iyya Da Yaki Da Cin Hanci Na 2025

Jagororin Jam'iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Sun Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki Da Ayyukan Jam'iyya Da Yaki Da Cin Hanci Na 2025

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.