ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Inuwar Gamji

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Inuwar gamji

Yayin da shekara ta 2024 ke ban kwana, tashe-tashen hankula da fitintinu na ci gaba da kazancewa. Shi kuma tattalin arzikin duniya yana ci gaba da tangal-tangal. Matsalar tsaro kuwa, wadda ta hada da ayyukan ta’addanci ta ki ci ta ki cinyewa, ballantana tabarbarewar yanayi wanda yake haddasa ambaliya, gobarar daji da dumamar yanayi, abin ba’a magana.

 

Wannan gagarumin kalubale ya sanya kasashe masu tasowa kasa cimma muradin Majalisar Dinkin Duniya (UN) na samu ci gaba mai dorewa ya zuwa shekara ta 2030. Wasu kasashen duniya kuwa, sabo da nuna isa da gadara, sun kekashe kan tsohon tsarin da suke a kai domin kare muradunsu na son zuciya.

ADVERTISEMENT
  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani
  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani

Kasar Sin, wadda tun fil azal ba ta yarda da cin zalun ba, ko nuna fin karfi domin biyan bukatunta, tana nan ba ta canza ba a kan manufarta ta gujewa tsoma baki a cikin harkokin cikin gida na kasashen da take ma’amala da su. “Cude ni in cude ka” shi ne babban tafarkin da kasar Sin take a kai a ma’amalarta da sauran kasashen duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

Idan ba’a manta ba dai, a watan Satumban wannan shekara ne Beijing ta shirya ta kuma aiwatar da gagarumin taron koli na hadin gwiwa tsakanin China da kasashen Afirka. A wajen taron ne, wanda ya samu halartar shugabanni da wakilan gwamnatocin kasashen Afirka su 53, har da shugaban kungiyar tarayyar Afirka, AU, aka cimma matsaya ta bai daya ta zurfafa dangantaka tsakanin China da Afirka, bisa tsarin ci gaban duniya.

 

Dukkan mahalarta taron bakinsu ya zo daya ta fuskar hada karfi domin aiwatar da tsarin daidaito, bin ka’ida da kuma bunkasa tattalin arzikin duniya, ta yadda kowa zai amfana.

 

Dalilin gagarumar nasarar taron koli na Beijing shi ne bayanin da China ta yi dalla dalla ba tare da rufa-rufa ba a kan manufarta ta kulla wannan dangantakar hadin gwiwa tsakaninta da kasashen Afirka. Hakan ya gamsar da mahalarta taron, kasancewar sun fahimci cewa kowa zai ci gajiyar wannan hadin gwiwa. Wannan ne ya ba su kwarin gwiwar sakin jiki tare da samun natsuwa da mahukuntan kasar ta China a matsayin aminai na gaskiya.

 

A watan Nuwamban da ya gabata ne, aka gudanar da taron koli na kungiyar hadin kan tattalin arziki na kasashen duniya da ake kira G20 a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil. Taron shi ne na farko tun lokacin da kungiyar tarayyar Afirka (AU) ta samu kasancewa mamba a cikin kungiyar biyo bayan taron kungiya ta G20 karo na 18 da aka gudanar a birnin New Delhi na India a watan satumban 2023, kungiyar AU ta samu shiga cikin kungiyar G20 a hukunce.

 

China ita ce ta yi ruwa ta yi tsaki wajen ganin kungiyar AU ta samu shiga kungiyar G20, sannan kuma ta tsaya tsayin daka wajen ganin kungiyar AU ta taka rawar gani a harkokin shugabanci na duniya.

 

Wannan shi ne ya kara jaddada kalaman shugaba Xi Jinping na kasar Sin na cewa babu yadda za’a samu ci gaba da daidaito a duniya yayin da masu hannu da shuni suke kara azurcewa, su kuma talakawa suke kara durmuyewa cikin kangin talauci.

 

Inuwar gamji
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Inuwar gamji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.