ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Inuwar Gamji

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Inuwar gamji

Yayin da shekara ta 2024 ke ban kwana, tashe-tashen hankula da fitintinu na ci gaba da kazancewa. Shi kuma tattalin arzikin duniya yana ci gaba da tangal-tangal. Matsalar tsaro kuwa, wadda ta hada da ayyukan ta’addanci ta ki ci ta ki cinyewa, ballantana tabarbarewar yanayi wanda yake haddasa ambaliya, gobarar daji da dumamar yanayi, abin ba’a magana.

 

Wannan gagarumin kalubale ya sanya kasashe masu tasowa kasa cimma muradin Majalisar Dinkin Duniya (UN) na samu ci gaba mai dorewa ya zuwa shekara ta 2030. Wasu kasashen duniya kuwa, sabo da nuna isa da gadara, sun kekashe kan tsohon tsarin da suke a kai domin kare muradunsu na son zuciya.

ADVERTISEMENT
  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani
  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani

Kasar Sin, wadda tun fil azal ba ta yarda da cin zalun ba, ko nuna fin karfi domin biyan bukatunta, tana nan ba ta canza ba a kan manufarta ta gujewa tsoma baki a cikin harkokin cikin gida na kasashen da take ma’amala da su. “Cude ni in cude ka” shi ne babban tafarkin da kasar Sin take a kai a ma’amalarta da sauran kasashen duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

Idan ba’a manta ba dai, a watan Satumban wannan shekara ne Beijing ta shirya ta kuma aiwatar da gagarumin taron koli na hadin gwiwa tsakanin China da kasashen Afirka. A wajen taron ne, wanda ya samu halartar shugabanni da wakilan gwamnatocin kasashen Afirka su 53, har da shugaban kungiyar tarayyar Afirka, AU, aka cimma matsaya ta bai daya ta zurfafa dangantaka tsakanin China da Afirka, bisa tsarin ci gaban duniya.

 

Dukkan mahalarta taron bakinsu ya zo daya ta fuskar hada karfi domin aiwatar da tsarin daidaito, bin ka’ida da kuma bunkasa tattalin arzikin duniya, ta yadda kowa zai amfana.

 

Dalilin gagarumar nasarar taron koli na Beijing shi ne bayanin da China ta yi dalla dalla ba tare da rufa-rufa ba a kan manufarta ta kulla wannan dangantakar hadin gwiwa tsakaninta da kasashen Afirka. Hakan ya gamsar da mahalarta taron, kasancewar sun fahimci cewa kowa zai ci gajiyar wannan hadin gwiwa. Wannan ne ya ba su kwarin gwiwar sakin jiki tare da samun natsuwa da mahukuntan kasar ta China a matsayin aminai na gaskiya.

 

A watan Nuwamban da ya gabata ne, aka gudanar da taron koli na kungiyar hadin kan tattalin arziki na kasashen duniya da ake kira G20 a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil. Taron shi ne na farko tun lokacin da kungiyar tarayyar Afirka (AU) ta samu kasancewa mamba a cikin kungiyar biyo bayan taron kungiya ta G20 karo na 18 da aka gudanar a birnin New Delhi na India a watan satumban 2023, kungiyar AU ta samu shiga cikin kungiyar G20 a hukunce.

 

China ita ce ta yi ruwa ta yi tsaki wajen ganin kungiyar AU ta samu shiga kungiyar G20, sannan kuma ta tsaya tsayin daka wajen ganin kungiyar AU ta taka rawar gani a harkokin shugabanci na duniya.

 

Wannan shi ne ya kara jaddada kalaman shugaba Xi Jinping na kasar Sin na cewa babu yadda za’a samu ci gaba da daidaito a duniya yayin da masu hannu da shuni suke kara azurcewa, su kuma talakawa suke kara durmuyewa cikin kangin talauci.

 

Inuwar gamji
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa
Inuwar gamji
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Noma Tsakanin Sin Da Afirka: Daga “Sari Ka Ba Ni” Zuwa ” Zamanintar Da Kansu Tare”

June 12, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 
Ra'ayi Riga

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya
Ra'ayi Riga

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa

LABARAI MASU NASABA

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.