• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Bai Wa Kowane Bangare Hakkinsa Daga Jawaban Shugaba Xi

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Kasar Sin Ke Bai Wa Kowane Bangare Hakkinsa Daga Jawaban Shugaba Xi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sau da yawa mutane kan yi mamakin irin hikimomin kasar Sin mai al’umma kusan biliyan daya da rabi ke amfani da su, wajen gudanar da al’amuranta, saboda yadda wasu ke cewa “idan dambu ya yi yawa, ba ya jin mai”.

 

Bari mu zakulo wasu daga cikin hikimomin da kasar ke amfani da su daga jawaban da Shugaba Xi Jinping ya gabatar a wurare da lokuta daban-daban.

  • Sarki Sanusi II Zai Sake Ayyana Wata Rana Ta Naɗa Sabon Hakimin Bichi
  • Kwamitin Ɗanyen Mai Ya Nuna Rashin Gamsuwa Da Jinkirin Haƙo Mai A Kolmani

Ga misalin farko game da nuna tausayin al’ummarta da kula da halin da jama’a za su shiga a kowane irin mataki da gwamnatin kasar za ta dauka.

 

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

A taron tattaunawar da aka yi da wakilan ’yan kasuwa da masana ilimi a ranar 23 ga Mayun 2024, Shugaba Xi ya ce, “Kamata ya yi a dauki matakan gyare-gyaren da za su magance matsalolin da suka fi damun al’umma da kuma saurare da aiwatar da abin da suke so, sannan a dauki kwararan matakai da za su samar da fa’ida ta hakika ga jama’a, da samun amincewarsu da mutunta ra’ayoyinsu gwargwadon iko, ta yadda gyare-gyaren da ake yi za su tabbatar da cikar burinsu da faranta musu rai da ba su cikakken tsaro.”

 

Ina da yakinin duk wanda ya sa kafa a kasar Sin, zai ga abubuwan da shugaban ya ambata a aikace.

 

Har ila yau, a dai wannan taron da wakilan ’yan kasuwa da masana ilimi, shugaban ya ce, “Yana da matukar muhimmanci a bi abubuwa sau da kafa da kuma inganta tsarin tattalin arzikin kasarmu, da gina babban tsari na tafiyar da tattalin arzikin kasuwanci bisa turbar gurguzu, da inganta tsarin kula da kananan sana’o’i da hanyoyin samar da ci gaba mai inganci.”

 

A nan, za a fahimci irin yadda kasar Sin take bin tsare-tsaren kawo ci gaba,da kyautata yanayin kasuwanci, da nuna ishara ga masana ilimi a kan ba da gudummawa wajen bayar da shawarwari a kan kula da kananan sana’o’i, da kawo hanyoyin samar da ci gaba mai inganci.

 

Kamar an tambayi Shugaba Xi, to ta yaya kasar Sin take aiwatar da tsare-tsarenta cikin nasara? A jawabin da ya gabatar a zaman nazari na rukuni-rukuni da aka yi lokacin taron sashin siyasa na Kwamitin Tsakiya na Jam’iyyar Kwaminis karo na 14, a ranar 27 ga Mayun 2024, ya ce, “Don magance matsalolin da suka shafi tsarin ayyukan yi da kawo ma’aikatan da ake bukatar a samar daidai da bukatu, ya kamata a yi kokarin hanzarta habaka samar da ma’aikata na zamani masu kwarewa da suka dace da zamani wadanda za su wadatar da kuma rarraba su a bisa ingantaccen tsari.”

 

Dangane da batun kimiyya da fasaha wanda duniya ke yi a zamanin nan, kasar Sin ta kasance jagora. Ga kuma daya daga cikin sirrukan kasar daga abin da Shugaba Xi ya ce a jawabinsa lokacin taron koli na kasa a kan kimiyya da fasaha da aka yi ranar 24 ga Yunin 2024, “Yana da matukar alfanu a sada tsakanin sabbin kirkire-kirkire na kimiyya da fasaha da kuma ci gaban masana’antu, ta yadda hakan zai taimaka wajen samar da sabbin ginshakai na kawo ci gaba.”

 

A bangaren muhalli kuwa, a halin yanzu kowa ya san yadda ake tataburza a tsakanin kasashe masu tasowa da masu karfin tattalin arziki game da gurbata muhalli, ta wannan fuskar ma, kasar Sin tana ci gaba da daukar matakai a cikin gida da yekuwar hakan a waje. Shugaba Xi ya bayyana hikimar kasar Sin a taron koli na kasar a kan kiyaye lafiyar muhalli, da ya gudana ranar 19 ga Yunin 2023, inda ya ce, “Ya kamata babban matakin kare muhalli da ake dauka ya taimaka wa kasar Sin ta ci gaba da samar da sabbin turaku da hanyoyin raya kasa, da kara himma ga gina tattalin arziki mara gurbata muhalli. Ta haka kasar za ta yi tsimin kudin da take yawan kashewa da rage gurbata muhalli yadda ya kamata, sannan za ta ci gaba da karfafa kokarinta na dorad da ci gaba.”

 

Daga wadannan misalai daga jawaban Shugaba Xi, ana iya fahimtar yadda kasar Sin ke bai wa ko wane bangare hakkinsa domin samun dorewar ci gaba, ba kawai ga kanta ba har ma da duniya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babu Wanda Zai Ci Nasara Daga Ayyukan Lalata Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Next Post

Matatar Ɗangote Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasar Kamaru

Related

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

16 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

17 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

18 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

19 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

20 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

2 days ago
Next Post
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Matatar Ɗangote Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasar Kamaru

LABARAI MASU NASABA

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.