ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
Kebbi

Hedkwatar ’Yansanda ta Jihar Kebbi ta kama wani da ake zargin dan ta’adda ne a yankin Illo, cikin Karamar Hukumar Bagudo ta jihar.

Haka kuma, rundunar ta kwato bindigogi biyu na gida da harsasai guda hudu a wani samame da aka kai bisa sahihan bayanan sirri.

  • Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, CSP Nafiu Abubakar, ya fitar a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Abubakar ya bayyana cewa an kama wanda ake zargin ne a ranar 9 ga Nuwamba, 2025, bayan wani sumame na gaggawa da Dibisional Police Officer (DPO) na Illo ya jagoranta bisa bayanan sirri masu inganci.

Ya ce an gudanar da aikin tare da hadin gwiwar ’yan sa kai a kauyen Tungar Gwani, inda aka kama wanda ake zargin mai suna Buba Garba, dan shekara 27, mazaunin kauyen Takalafiya da ke Karamar Hukumar Suru.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

“Da zarar wanda ake zargin ya hango jami’an, ya yi amfani da wuka ya yanki daya daga cikin ’yan sa kai a kugu da hannu, wanda hakan ya jikkata shi sosai,” in ji mai magana da yawun ’yansandan.

Ya kara da cewa an garzaya da dan sa kai da ya ji rauni zuwa cibiyar lafiya mafi kusa, inda yake karbar magani a halin yanzu.

Bayan binciken jiki da aka yi wa wanda ake zargi, jami’an sun samu bindiga daya ta gida, bindiga daya, da kuma harsasai guda hudu a hannunsa.

A cikin martaninsa, kwamishinan ’yansandan jihar, CP Bello Sani, ya yaba da kwararrun ayyuka da dabarun binciken bayanan sirri da kuma hadin kai tsakanin DPO na Illo da tawagarsa tare da ’yan sa kai na yankin.

Ya ce, “Ina yabawa da yadda sashen Illo suka yi aiki cikin gaggawa da hadin kai. Wannan aikin ya nuna cewa idan hukumomin tsaro da al’umma suka hada kai, masu aikata laifi ba za su samu damar tserewa ba.”

Haka kuma, kwamishinan ya umurci a mika shari’ar zuwa sashen binciken masu laifi (SCID) na jihar da ke Birnin Kebbi domin ci gaba da bincike mai zurfi, da nufin gano cibiyar hadin gwiwar wanda ake zargi da yadda yake gudanar da ayyukansa, tare da kamo abokan aikinsa.

Ya ce, “’Yan sanda kadai ba za su iya cin nasara a wannan yaki ba. Muna bukatar ci gaba da samun goyon bayan jama’a ta hanyar bayar da bayanai cikin lokaci da kuma sahihai.”

Rundunar ta kuma tabbatar da aniyarta wajen kara kaimi a yaki da ’yan bindiga da sauran nau’o’in laifukan tashin hankali a fadin jihar, tare da tabbatar wa jama’a cewa an dauki matakan rigakafi domin kare rayukansu da dukiyoyinsu.

idan za a tunawa a watan Oktoba, jaridar The PUNCH ta ruwaito cewa rundunar ’yan sandan Jihar Kano ta kama wasu mutum biyu da ake zargi da kasancewa ’yan kungiyar ’yan bindiga.

Kwamishinan ’yan sanda na jihar, Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cewa an kama su ne yayin wata hadin gwiwar sumame da jami’an Anti-Kidnapping Skuad da na Sashen Shanono Dibision suka gudanar da misalin karfe 2 na safe, bayan samun sahihan bayanai daga mazauna kauyen Farin Ruwa a Karamar Hukumar Shanono.

Ya kara da cewa ana zargin wadanda aka kama suna hadin gwiwa da ’yan bindigar da ke kokarin shiga cikin Jihar Kano, inda ya bayyana cewa an fara bincike domin gano tsarin hadin gwiwarsu da kuma kama sauran mambobin kungiyar.

Kebbi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.