ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

by Rabi'u Ali Indabawa
8 months ago
Kebbi

Hedkwatar ’Yansanda ta Jihar Kebbi ta kama wani da ake zargin dan ta’adda ne a yankin Illo, cikin Karamar Hukumar Bagudo ta jihar.

Haka kuma, rundunar ta kwato bindigogi biyu na gida da harsasai guda hudu a wani samame da aka kai bisa sahihan bayanan sirri.

  • Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, CSP Nafiu Abubakar, ya fitar a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Abubakar ya bayyana cewa an kama wanda ake zargin ne a ranar 9 ga Nuwamba, 2025, bayan wani sumame na gaggawa da Dibisional Police Officer (DPO) na Illo ya jagoranta bisa bayanan sirri masu inganci.

Ya ce an gudanar da aikin tare da hadin gwiwar ’yan sa kai a kauyen Tungar Gwani, inda aka kama wanda ake zargin mai suna Buba Garba, dan shekara 27, mazaunin kauyen Takalafiya da ke Karamar Hukumar Suru.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

“Da zarar wanda ake zargin ya hango jami’an, ya yi amfani da wuka ya yanki daya daga cikin ’yan sa kai a kugu da hannu, wanda hakan ya jikkata shi sosai,” in ji mai magana da yawun ’yansandan.

Ya kara da cewa an garzaya da dan sa kai da ya ji rauni zuwa cibiyar lafiya mafi kusa, inda yake karbar magani a halin yanzu.

Bayan binciken jiki da aka yi wa wanda ake zargi, jami’an sun samu bindiga daya ta gida, bindiga daya, da kuma harsasai guda hudu a hannunsa.

A cikin martaninsa, kwamishinan ’yansandan jihar, CP Bello Sani, ya yaba da kwararrun ayyuka da dabarun binciken bayanan sirri da kuma hadin kai tsakanin DPO na Illo da tawagarsa tare da ’yan sa kai na yankin.

Ya ce, “Ina yabawa da yadda sashen Illo suka yi aiki cikin gaggawa da hadin kai. Wannan aikin ya nuna cewa idan hukumomin tsaro da al’umma suka hada kai, masu aikata laifi ba za su samu damar tserewa ba.”

Haka kuma, kwamishinan ya umurci a mika shari’ar zuwa sashen binciken masu laifi (SCID) na jihar da ke Birnin Kebbi domin ci gaba da bincike mai zurfi, da nufin gano cibiyar hadin gwiwar wanda ake zargi da yadda yake gudanar da ayyukansa, tare da kamo abokan aikinsa.

Ya ce, “’Yan sanda kadai ba za su iya cin nasara a wannan yaki ba. Muna bukatar ci gaba da samun goyon bayan jama’a ta hanyar bayar da bayanai cikin lokaci da kuma sahihai.”

Rundunar ta kuma tabbatar da aniyarta wajen kara kaimi a yaki da ’yan bindiga da sauran nau’o’in laifukan tashin hankali a fadin jihar, tare da tabbatar wa jama’a cewa an dauki matakan rigakafi domin kare rayukansu da dukiyoyinsu.

idan za a tunawa a watan Oktoba, jaridar The PUNCH ta ruwaito cewa rundunar ’yan sandan Jihar Kano ta kama wasu mutum biyu da ake zargi da kasancewa ’yan kungiyar ’yan bindiga.

Kwamishinan ’yan sanda na jihar, Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cewa an kama su ne yayin wata hadin gwiwar sumame da jami’an Anti-Kidnapping Skuad da na Sashen Shanono Dibision suka gudanar da misalin karfe 2 na safe, bayan samun sahihan bayanai daga mazauna kauyen Farin Ruwa a Karamar Hukumar Shanono.

Ya kara da cewa ana zargin wadanda aka kama suna hadin gwiwa da ’yan bindigar da ke kokarin shiga cikin Jihar Kano, inda ya bayyana cewa an fara bincike domin gano tsarin hadin gwiwarsu da kuma kama sauran mambobin kungiyar.

Kebbi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.