ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
Fashi

An yanke wa ’yan Nijeriya hudu da ke cikin wata kungiyar fashi ta wayoyi da ta addabi birnin Landan hukuncin daurin shekaru 55 gaba daya, a kotun Kingston Crown Court da ke Birtaniya.

Jaridar PUNCH Metro ta samo wannan bayanin ne daga wata sanarwa da aka wallafa a shafin Intanet UK Metropolitan Police a ranar Litinin.

  • BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani
  • Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

A cewar sanarwar, wadanda aka yanke wa hukuncin sun hada da Dabid Akintola, Ayomide Olaribiro, Olabiyi Obasa, da Dabid Okewole.

ADVERTISEMENT

Sauran da ke cikin kungiyar sun hada da James Adodo, Robert Hills, Nelson Joel, Michael Babo, Mushtakim Miah, da Labille Bloise.

Sanarwar ta bayyana cewa tsakanin Satumba da Nuwamba 2024, kungiyar ta gudanar da akalla fashi 13 a shagunan waya daban-daban a fadin Birtaniya.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Ta ce, “Kungiyar ta fi kai hare-hare a shagunan EE, inda suke amfani da barazana da tashin hankali wajen tilasta ma’aikata su bude dakunan ajiya na sirri kafin su gudu da wayoyi masu tsada da sauran na’urori.”

A jimlace, sun sace kayayyaki da darajarsu ta kai fam miliyan £240,000.

Jami’an tsaro sun gano masu laifin ta hanyar shaidar DNA, da kuma bayanan kira da rikodin motocin da suka yi amfani da su.

An ce sun ci gaba da bibiyar kungiyar yayin da take shirin sake kai wani hari, inda a ranar 19 ga Nuwamba, 2024, jami’ai suka yi musu kwanton bauna suka kama mutane hudu daga cikinsu a lokacin da suke kokarin yin fashi a wani shagon EE da ke Kilburn.

“Bincike a gidajen da ake danganta su da wadanda ake zargin ya kai ga gano kayan da aka sace da karin shaidu da ke hada kungiyar da fashi-fashin.”

Sanarwar ta bayyana cewa mutane 10 da aka kama a lokacin aikin an gurfanar da su a kotu, inda takwas suka amsa laifi na hadin gwiwa wajen fashi a ranar 30 ga Janairu.

Sanarwar ta kara da cewa bayan amsa laifin, an yanke musu hukuncin a ranar Jumma’a, 7 ga Nuwamba.

Ta bayyana tsawon lokacin da za su yi a gidan yari kamar haka:

James Adodo na St Martins Road, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 10 a gidan yari.

Dabid Akintola na Samuel Street, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 6 da watanni 6 a gidan yari.

Michael Babo na Gilbert Close, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 6 da watanni 10 a gidan yari.

Robert Hills na Mayfield Road, Grabesend, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 5 da watanni 3 a gidan yari.

Ayomide Olaribiro na Warrior Skuare, Manor Park, an yanke masa hukuncin shekaru 4 da watanni 6 a gidan yari.

Nelson Joel na St Martins Road, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 3 da watanni 3 a gidan yari.

Olabiyi Obasa na Norfolk Close, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 3 da watanni 6 a gidan yari.

Dabid Okewole na Bale Road, Northfleet, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 7 da watanni 6 a gidan yari.

Sanarwar ta kuma nuna cewa wasu da aka yi kara biyu sun amsa laifin kokarin fashi, inda aka yanke musu hukuncin da ya dace.

Labille Bloise na Goldcrest Close, Thamesmead, an yanke masa hukuncin shekaru 2, wanda aka dage har tsawon shekaru 2.

Mushtakim Miah na Artillery Place, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 8 da watanni 6 a gidan yari.

Wannan shari’a ta zo ne a daidai lokacin da ake karuwa da rahotannin ’yan Nijeriya da ke kasashen waje da ake yanke musu hukuncin laifuka.

Jaridar PUNCH Metro ta ruwaito a ranar Laraba da ta gabata cewa wani dalibi dan Nijeriya mai digiri na biyu da ke zaune a Birtaniya, Chiemka Okoronta, zai yi kaura daga kasar bayan ya yi zaman gidan yari na shekaru 10, saboda an same shi da laifin fyade kan wata yarinya.

Fashi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.