ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
Fashi

An yanke wa ’yan Nijeriya hudu da ke cikin wata kungiyar fashi ta wayoyi da ta addabi birnin Landan hukuncin daurin shekaru 55 gaba daya, a kotun Kingston Crown Court da ke Birtaniya.

Jaridar PUNCH Metro ta samo wannan bayanin ne daga wata sanarwa da aka wallafa a shafin Intanet UK Metropolitan Police a ranar Litinin.

  • BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani
  • Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

A cewar sanarwar, wadanda aka yanke wa hukuncin sun hada da Dabid Akintola, Ayomide Olaribiro, Olabiyi Obasa, da Dabid Okewole.

ADVERTISEMENT

Sauran da ke cikin kungiyar sun hada da James Adodo, Robert Hills, Nelson Joel, Michael Babo, Mushtakim Miah, da Labille Bloise.

Sanarwar ta bayyana cewa tsakanin Satumba da Nuwamba 2024, kungiyar ta gudanar da akalla fashi 13 a shagunan waya daban-daban a fadin Birtaniya.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Ta ce, “Kungiyar ta fi kai hare-hare a shagunan EE, inda suke amfani da barazana da tashin hankali wajen tilasta ma’aikata su bude dakunan ajiya na sirri kafin su gudu da wayoyi masu tsada da sauran na’urori.”

A jimlace, sun sace kayayyaki da darajarsu ta kai fam miliyan £240,000.

Jami’an tsaro sun gano masu laifin ta hanyar shaidar DNA, da kuma bayanan kira da rikodin motocin da suka yi amfani da su.

An ce sun ci gaba da bibiyar kungiyar yayin da take shirin sake kai wani hari, inda a ranar 19 ga Nuwamba, 2024, jami’ai suka yi musu kwanton bauna suka kama mutane hudu daga cikinsu a lokacin da suke kokarin yin fashi a wani shagon EE da ke Kilburn.

“Bincike a gidajen da ake danganta su da wadanda ake zargin ya kai ga gano kayan da aka sace da karin shaidu da ke hada kungiyar da fashi-fashin.”

Sanarwar ta bayyana cewa mutane 10 da aka kama a lokacin aikin an gurfanar da su a kotu, inda takwas suka amsa laifi na hadin gwiwa wajen fashi a ranar 30 ga Janairu.

Sanarwar ta kara da cewa bayan amsa laifin, an yanke musu hukuncin a ranar Jumma’a, 7 ga Nuwamba.

Ta bayyana tsawon lokacin da za su yi a gidan yari kamar haka:

James Adodo na St Martins Road, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 10 a gidan yari.

Dabid Akintola na Samuel Street, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 6 da watanni 6 a gidan yari.

Michael Babo na Gilbert Close, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 6 da watanni 10 a gidan yari.

Robert Hills na Mayfield Road, Grabesend, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 5 da watanni 3 a gidan yari.

Ayomide Olaribiro na Warrior Skuare, Manor Park, an yanke masa hukuncin shekaru 4 da watanni 6 a gidan yari.

Nelson Joel na St Martins Road, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 3 da watanni 3 a gidan yari.

Olabiyi Obasa na Norfolk Close, Dartford, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 3 da watanni 6 a gidan yari.

Dabid Okewole na Bale Road, Northfleet, Kent, an yanke masa hukuncin shekaru 7 da watanni 6 a gidan yari.

Sanarwar ta kuma nuna cewa wasu da aka yi kara biyu sun amsa laifin kokarin fashi, inda aka yanke musu hukuncin da ya dace.

Labille Bloise na Goldcrest Close, Thamesmead, an yanke masa hukuncin shekaru 2, wanda aka dage har tsawon shekaru 2.

Mushtakim Miah na Artillery Place, Woolwich, an yanke masa hukuncin shekaru 8 da watanni 6 a gidan yari.

Wannan shari’a ta zo ne a daidai lokacin da ake karuwa da rahotannin ’yan Nijeriya da ke kasashen waje da ake yanke musu hukuncin laifuka.

Jaridar PUNCH Metro ta ruwaito a ranar Laraba da ta gabata cewa wani dalibi dan Nijeriya mai digiri na biyu da ke zaune a Birtaniya, Chiemka Okoronta, zai yi kaura daga kasar bayan ya yi zaman gidan yari na shekaru 10, saboda an same shi da laifin fyade kan wata yarinya.

Fashi
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.