• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Cututtuka 8 Da Ke Kama Zomo Da Hanyoyin Mangance Su

by Abubakar Abba
10 months ago
Cututtuka

Zomo dabba ce da ke da saurin sabo da jama’a, kana kuma namansa na da matukar dadi tare da karawa jikin Dan’adam lafiya, musamman duba da cewa, yana dauke da ‘sinadarin protein’.

Saboda haka, yana da kyau ga mai kiwan sa; ya rika ba shi kulawa yadda ya kamata tare kuma da sanin lokacin da yake sauya dab’arsa.

  • Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa
  • Cimma Burin Rage Salwantar Abinci A Kasar Sin Zai Samar Da Mafita Ga Duniya

Akwai cututtuka takwas da ka iya harbin Zomo da kuma hanyoyin magance su.

1- Harbi A Kunne:

Akwai wata cuta da a turance ake kira da ‘mites’ da ke harbin sa a kunne, wadda take sanya masa jin kaikayi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Ana magance wannan cuta ne, ta hanyar yawan duba kunnen nasa a kullum; don ba shi kariyar da ta kamata.

Kazalka, ana yakar cutar ne; ta hanyar rika shafa masa mai a wurin da cutar ta harbe shi.

2- Cutar Da Ke Fito Masa A Kan Hanci:

Akasari wannan cuta da a turance ake kiran ta da ‘Snuffles Rabbit’, ta na fito masa ne a kan Hanci; wanda hakan ke sanya wa yake fitar da majina ko kuma Idonsa ya rika fitar da ruwa.

Ana dakile wannan cuta, ta hanyar ciyar da Zomon abinci mai gina jiki tare kuma da tabbatar da ana tsaftace wajen kwanansa.

3- Tsananin Zafin Da Ke Rage Masa Kuzari:

Wannan cuta wacce a turance ake kira da ‘Heat Stroke’, na sanya masa rashin walwala; ana kuma so mai kiwon sa ya tabbatar yana lura da wannan cuta.

Ana dakile cutar ne, ta hanyar ajiye Zomon a cikin inuwa tare da kare shi da ajiye shi a cikin hasken rana.

4- Cutar Da Ke Harbin Sa A Kafa:

Idan ka lura da wannan cuta, wacce a turance ake kira da ‘Sore Hocks’, za ka ga Zomon yana jin zafi a kafarsa, sannan kuma a cikin sauki, ana iya warkar da ita.

Ana kare shi daga kamuwa da wannan cuta, ta hanyar sanya masa raga a wajen barcinsa ko kuma sanya masa tabarma; don ya rika dora kafarsa.

5- Cutar Da Ke Harbin ‘Ya’yan Hanjinsa:

Wannan cuta da ake kira ‘Bloat’, idan ta harbi Zomo tana yin sanadiyyar mutuwar sa; ana kuma yawan samun ta tare da Zomaye.

Kazalika, cutar tana sanya masa kumburin jiki.

Ana dakile ta ne kuma ta hanyar yawan duba yanayin da Zomon yake gudanar da rayuwarsa.

6- Cutar ‘Coccidiosis’:

Wata cuta sananniya ce wadda ke harbin Zomo, tana farauwa ne idan Zomon ya fara yin gudawa, inda cutar ke shafar hantar Zomon da ya kamu, inda kuma cutar ke hana su cin abinci da kasa shan ruwa.

7- Cutar Da Ke Sanya Kan Zomo Ko Wuyansa Yawan Kadawa:

Wannan cuta da ake kira ‘Head Tilt’, sananniya ce da ke harbin Zomo.

8- Fitsarinsa Na Komawa Ja:

Akwai cutar da ke harbin sa, wacce ke sany fitsarinsa ya koma ja ko ruwan dorawa.

Don haka, idan mai kiwon ya ga haka; kada ya ji tsoro mai yiwuwa yana cin abinci ne da yawa kamar Karas.

Sai dai, idan yana samun sauyin abinci ko kuma sun ci gaba da yin irin wannan kalar fitsari, bayan an sauya masa abincin ana bukatar mai kiwon ya dauki wani nau’i na fitsarin nasa; don yin gwaji.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
Tsaro

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22

October 12, 2025
Next Post
Gobara Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Magidanci Da Matarsa A Kano

Gobara Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Magidanci Da Matarsa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

October 22, 2025
Tanka

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025
Zimbabwe Ta Jinjinawa Jarin Sin A Matsayin Wanda Ya Bunkasa Masana’atun Samar Da Siminti A Kasar

Zimbabwe Ta Jinjinawa Jarin Sin A Matsayin Wanda Ya Bunkasa Masana’atun Samar Da Siminti A Kasar

October 22, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

Gwamna Uba Sani Ya Rantsar Da Sabon Kwamishinan Yada Labarai Ahmed Maiyaki 

October 22, 2025
Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

Ba A Yi Wa Kiristoci Kisan Gilla A Arewacin Nijeriya – Sarkin Musulmi

October 22, 2025
Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025 Na Jaridar Leadership: Dauda Lawal

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.