• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Cututtuka 8 Da Ke Kama Zomo Da Hanyoyin Mangance Su

by Abubakar Abba
7 months ago
in Tsaro
0
Nazari Kan Cututtuka 8 Da Ke Kama Zomo Da Hanyoyin Mangance Su
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zomo dabba ce da ke da saurin sabo da jama’a, kana kuma namansa na da matukar dadi tare da karawa jikin Dan’adam lafiya, musamman duba da cewa, yana dauke da ‘sinadarin protein’.

Saboda haka, yana da kyau ga mai kiwan sa; ya rika ba shi kulawa yadda ya kamata tare kuma da sanin lokacin da yake sauya dab’arsa.

  • Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa
  • Cimma Burin Rage Salwantar Abinci A Kasar Sin Zai Samar Da Mafita Ga Duniya

Akwai cututtuka takwas da ka iya harbin Zomo da kuma hanyoyin magance su.

1- Harbi A Kunne:

Akwai wata cuta da a turance ake kira da ‘mites’ da ke harbin sa a kunne, wadda take sanya masa jin kaikayi.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Ana magance wannan cuta ne, ta hanyar yawan duba kunnen nasa a kullum; don ba shi kariyar da ta kamata.

Kazalka, ana yakar cutar ne; ta hanyar rika shafa masa mai a wurin da cutar ta harbe shi.

2- Cutar Da Ke Fito Masa A Kan Hanci:

Akasari wannan cuta da a turance ake kiran ta da ‘Snuffles Rabbit’, ta na fito masa ne a kan Hanci; wanda hakan ke sanya wa yake fitar da majina ko kuma Idonsa ya rika fitar da ruwa.

Ana dakile wannan cuta, ta hanyar ciyar da Zomon abinci mai gina jiki tare kuma da tabbatar da ana tsaftace wajen kwanansa.

3- Tsananin Zafin Da Ke Rage Masa Kuzari:

Wannan cuta wacce a turance ake kira da ‘Heat Stroke’, na sanya masa rashin walwala; ana kuma so mai kiwon sa ya tabbatar yana lura da wannan cuta.

Ana dakile cutar ne, ta hanyar ajiye Zomon a cikin inuwa tare da kare shi da ajiye shi a cikin hasken rana.

4- Cutar Da Ke Harbin Sa A Kafa:

Idan ka lura da wannan cuta, wacce a turance ake kira da ‘Sore Hocks’, za ka ga Zomon yana jin zafi a kafarsa, sannan kuma a cikin sauki, ana iya warkar da ita.

Ana kare shi daga kamuwa da wannan cuta, ta hanyar sanya masa raga a wajen barcinsa ko kuma sanya masa tabarma; don ya rika dora kafarsa.

5- Cutar Da Ke Harbin ‘Ya’yan Hanjinsa:

Wannan cuta da ake kira ‘Bloat’, idan ta harbi Zomo tana yin sanadiyyar mutuwar sa; ana kuma yawan samun ta tare da Zomaye.

Kazalika, cutar tana sanya masa kumburin jiki.

Ana dakile ta ne kuma ta hanyar yawan duba yanayin da Zomon yake gudanar da rayuwarsa.

6- Cutar ‘Coccidiosis’:

Wata cuta sananniya ce wadda ke harbin Zomo, tana farauwa ne idan Zomon ya fara yin gudawa, inda cutar ke shafar hantar Zomon da ya kamu, inda kuma cutar ke hana su cin abinci da kasa shan ruwa.

7- Cutar Da Ke Sanya Kan Zomo Ko Wuyansa Yawan Kadawa:

Wannan cuta da ake kira ‘Head Tilt’, sananniya ce da ke harbin Zomo.

8- Fitsarinsa Na Komawa Ja:

Akwai cutar da ke harbin sa, wacce ke sany fitsarinsa ya koma ja ko ruwan dorawa.

Don haka, idan mai kiwon ya ga haka; kada ya ji tsoro mai yiwuwa yana cin abinci ne da yawa kamar Karas.

Sai dai, idan yana samun sauyin abinci ko kuma sun ci gaba da yin irin wannan kalar fitsari, bayan an sauya masa abincin ana bukatar mai kiwon ya dauki wani nau’i na fitsarin nasa; don yin gwaji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciZomo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan

Next Post

Gobara Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Magidanci Da Matarsa A Kano

Related

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja
Tsaro

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

5 days ago
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u
Tsaro

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

1 week ago
Sojoji Sun DaÆ™ile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina
Tsaro

Sojoji Sun DaÆ™ile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

2 weeks ago
Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato
Tsaro

Sojoji Sun Damƙe Ɗan Fashi, Sun Kwato Makamai A Kaduna Da Filato

2 weeks ago
Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
Tsaro

Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina

3 weeks ago
Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona Gidaje
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona Gidaje

3 weeks ago
Next Post
Gobara Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Magidanci Da Matarsa A Kano

Gobara Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Magidanci Da Matarsa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

July 2, 2025
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

July 2, 2025
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

July 2, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

July 2, 2025
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.