ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Cututtuka 8 Da Ke Kama Zomo Da Hanyoyin Mangance Su

by Abubakar Abba
2 years ago
Cututtuka

Zomo dabba ce da ke da saurin sabo da jama’a, kana kuma namansa na da matukar dadi tare da karawa jikin Dan’adam lafiya, musamman duba da cewa, yana dauke da ‘sinadarin protein’.

Saboda haka, yana da kyau ga mai kiwan sa; ya rika ba shi kulawa yadda ya kamata tare kuma da sanin lokacin da yake sauya dab’arsa.

  • Jan Kafar Tinubu Na Cire Harajin Shigo Da Abinci Na Ci Gaba Da Ta’azzara rayuwa
  • Cimma Burin Rage Salwantar Abinci A Kasar Sin Zai Samar Da Mafita Ga Duniya

Akwai cututtuka takwas da ka iya harbin Zomo da kuma hanyoyin magance su.

ADVERTISEMENT

1- Harbi A Kunne:

Akwai wata cuta da a turance ake kira da ‘mites’ da ke harbin sa a kunne, wadda take sanya masa jin kaikayi.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Ana magance wannan cuta ne, ta hanyar yawan duba kunnen nasa a kullum; don ba shi kariyar da ta kamata.

Kazalka, ana yakar cutar ne; ta hanyar rika shafa masa mai a wurin da cutar ta harbe shi.

2- Cutar Da Ke Fito Masa A Kan Hanci:

Akasari wannan cuta da a turance ake kiran ta da ‘Snuffles Rabbit’, ta na fito masa ne a kan Hanci; wanda hakan ke sanya wa yake fitar da majina ko kuma Idonsa ya rika fitar da ruwa.

Ana dakile wannan cuta, ta hanyar ciyar da Zomon abinci mai gina jiki tare kuma da tabbatar da ana tsaftace wajen kwanansa.

3- Tsananin Zafin Da Ke Rage Masa Kuzari:

Wannan cuta wacce a turance ake kira da ‘Heat Stroke’, na sanya masa rashin walwala; ana kuma so mai kiwon sa ya tabbatar yana lura da wannan cuta.

Ana dakile cutar ne, ta hanyar ajiye Zomon a cikin inuwa tare da kare shi da ajiye shi a cikin hasken rana.

4- Cutar Da Ke Harbin Sa A Kafa:

Idan ka lura da wannan cuta, wacce a turance ake kira da ‘Sore Hocks’, za ka ga Zomon yana jin zafi a kafarsa, sannan kuma a cikin sauki, ana iya warkar da ita.

Ana kare shi daga kamuwa da wannan cuta, ta hanyar sanya masa raga a wajen barcinsa ko kuma sanya masa tabarma; don ya rika dora kafarsa.

5- Cutar Da Ke Harbin ‘Ya’yan Hanjinsa:

Wannan cuta da ake kira ‘Bloat’, idan ta harbi Zomo tana yin sanadiyyar mutuwar sa; ana kuma yawan samun ta tare da Zomaye.

Kazalika, cutar tana sanya masa kumburin jiki.

Ana dakile ta ne kuma ta hanyar yawan duba yanayin da Zomon yake gudanar da rayuwarsa.

6- Cutar ‘Coccidiosis’:

Wata cuta sananniya ce wadda ke harbin Zomo, tana farauwa ne idan Zomon ya fara yin gudawa, inda cutar ke shafar hantar Zomon da ya kamu, inda kuma cutar ke hana su cin abinci da kasa shan ruwa.

7- Cutar Da Ke Sanya Kan Zomo Ko Wuyansa Yawan Kadawa:

Wannan cuta da ake kira ‘Head Tilt’, sananniya ce da ke harbin Zomo.

8- Fitsarinsa Na Komawa Ja:

Akwai cutar da ke harbin sa, wacce ke sany fitsarinsa ya koma ja ko ruwan dorawa.

Don haka, idan mai kiwon ya ga haka; kada ya ji tsoro mai yiwuwa yana cin abinci ne da yawa kamar Karas.

Sai dai, idan yana samun sauyin abinci ko kuma sun ci gaba da yin irin wannan kalar fitsari, bayan an sauya masa abincin ana bukatar mai kiwon ya dauki wani nau’i na fitsarin nasa; don yin gwaji.

Cututtuka
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Gobara Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Magidanci Da Matarsa A Kano

Gobara Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Magidanci Da Matarsa A Kano

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.