• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: ‘Yan Majalisan Adawa 18 Suka Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC ta kara samun tagomashi a daidai lokacin da ‘yan majalisan adawa na jam’iyyun PDP da LP suka sauya sheka zuwa APC mai mulki.

Jam’iyya mai mulki na ta kara karfi, yayin da jam’iyyun adawa ke kara samun rikicin cikin gida gabanin zaben 2027.

  • Yadda Sin Da Kasashen Afirka Ke Hadin Gwiwar Zamanantar Da Ayyukan Noma
  • Mun Karbi Rancen Dala Biliyan 1 Don Tallafa Wa Matatar Man Dangote —NNPC

A yayin da zaben 2027 ke kara karatowa, ana kara rage kima da martabar jam’iyyun adawa, musamman jam’iyyar LP da kuma PDP.

Yayin da jam’iyyar PDP ke fama da rigingimun cikin gida wanda ya kai ga ficewar wasu ‘ya’yan jam’iyyar, a halin yanzu jam’iyyar LP ce ta fi fama da rikicin cikin gida, inda ta aka fi samun sauyin sheka a tsakanin ‘ya’yanta.

A cewar manazarta, sauya shekar da ke ci gaba da gudana tun bayan fara zaman majalisar dokokin kasar nan karo na 10 a shekarar 2023, tuni aka fara samun gagarumin tasiri a siyasance, musamman ga irin tasirin da jam’iyyar ke da shi da kuma tsayuwar daka a majalisun tarayya guda biyu.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Tun bayan kaddamar da majalisa ta 10, jam’iyyar LP tana da ‘yan majalisa ‘yan tsiraru a zauren majalisan kasar nan.

Kamar yadda sakamakon zaben 2023 ya nuna, jam’iyyar ta samu kujeru 35 a majalisar wakilai, wanda hakan ya samu karin girma daga zabukan da suka gabata, saboda farin jinin dan takararta na shugaban kasa, Mista Peter Obi, da kuma yadda jam’iyyar ta mayar da hankali kan matasa da kawo sauyi.

Wannan adadin kujeru na wakiltar ya kara wa jam’iyyar kima, inda ya sanya ta a matsayin wata jigo a majalisar.

Sai dai jam’iyyar LP ta sha ganin ficewar mambobinta zuwa wasu jam’iyyun siyasa, musamman jam’iyyar APC mai mulki da kuma babbar jam’iyyar adawa ta PDP.

‘Yan majalisar da suka jefar da LP sun hada da Tochukwu Okere (Imo), Donatus Mathew (Kaduna), Bassey Akiba (Kuros Ribas), Iyawe Esosa (Edo) da Daulyop Fom (Filato).

Wannan yunkurin ya rage karfin lambobin LP a cikin zauren majalisa.

A ranar 12 ga watan Disamba, 2024, adadin mambobin jam’iyyar a majalisar wakiali ya ragu daga 35 zuwa 17, wanda hakan ke nufin jam’iyyar ta yi asarar kujeru 18 a cikin shekara daya da rabi.

A majalisar dattawa kuwa, Sanata Francis Onyewuchi, wanda ya wakilci Imo ta Gabas a karkashin jam’iyyar LP, shi ma ya fice daga jam’iyyar zuwa APC.

Rikicin cikin gida da ke tsakanin manyan jiga-jigan jam’iyyar LP a matakin kasa da kuma zargin kutsawa da wakilan jam’iyyar APC mai mulki ke yi babu shakka ya taka rawa a cikin abubuwan da ke na sauya sheka.

Ita kuwa jam’iyyar adawa ta PDP ta rasa Hon. Erhiatake Ibori-Suenu, mamba mai wakiltar mazabar Ethiope ta Jihar Delta, inda ta sauya sheka zuwa APC.

Ga dukkan alamu an fara cin PDP da yaki. Mambobin kwamitin gudanarwa wadanda ke da alhakin gudanar da ayyukan yau da kullum na jam’iyyar, har yanzu ba su gama farfadowa ba daga yakin da ake yi na kaka-nika-yi da ya yi sanadin tarwatsa jam’iyyar.

Sakamakon haka, yayin da shugabannin jam’iyyar masu goyon bayan tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ke murnar kiran da kwamitin amintattu (BoT) ya yi na a samar da wanda zai maye gurbin tsohon shugaban jam’iyyar na kasa, Iyorchia Ayu, wadanda muradinsu ya yi daidai da na ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, na shirin ci gaba da rike mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Amb. Umar Damagum, a ofis.

Wike, wanda shi ne shugaban gwamnonin G-5, kungiyar gwamnonin PDP da suka taka rawa a yunkurin jam’iyyar na neman mulki da Bola Tinubu a 2023, sun ci gaba da zama a cikin jam’iyyar kuma da alama za su yi wa Tinubu aiki a karo na biyu a 2027.

An tabbatar da cewa ajiye Damagum a ofis har zuwa Disamba 2025 lokacin da wa’adin Ayu ya kare a hukumance zai biya bukatun bangaren su Wike.

Domin cimma manufofinsa, ya zuwa yanzu wannan bangaren Wike ya yi nasarar sauya taron kwamitin zartaswa na kasa na jam’iyyar zuwa wani matsayi sau uku a jere tun daga watan Maris din 2024, wanda hakan ya tsawaita zamansa.

Ana sa ran za a yanke shawara kan ko za a zabi sabon shugaban jam’iyyar ko kuma Damagum za a bar shi ya ci gaba da aiki a taron na kwamitin zartarwa na jam’iyyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC, ICPC Sun Kwato Naira Biliyan 277.69 Da Dala Miliyan 106 A Shekara Guda

Next Post

Sin Da Amurka Za Su Iya Samar Da Alfanu Ga Duniya a Hadin Gwiwarsu

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Sin Da Amurka Za Su Iya Samar Da Alfanu Ga Duniya a Hadin Gwiwarsu

Sin Da Amurka Za Su Iya Samar Da Alfanu Ga Duniya a Hadin Gwiwarsu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

July 3, 2025
Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

July 3, 2025
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

July 3, 2025
Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

July 3, 2025
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

July 3, 2025
Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

July 3, 2025
Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

July 3, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3

July 3, 2025
Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

July 3, 2025
Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.