• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kudin Kirifto: An Cafke Dan Nijeriya Da Laifin Damfarar ‘Yan Australiya Dala Miliyan 8

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Kudin Kirifto: An Cafke Dan Nijeriya Da Laifin Damfarar ‘Yan Australiya Dala Miliyan 8
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) sun kama Osang Usie Otukpa, wani dan Nijeriya da ake zargi ya damfari wasu ‘yan kasar Australia 139 Dala miliyan 8 ta hanyar kudin Kirifto.

An kama wanda ake zargin ne a filin jirgin sama na Murtala Mohammed da ke Ikeja a Legas, lokacin da ya fito daga kasar Amurka.

  • Yahaya Bello Ya Samu Beli Bayan Cika Sharudan Kotu
  • EU Ta Ware Euro Miliyan 1 Don Tallafa Wa Wadanda Ambaliyar Ruwa Da Kwalara Suka Shafa A Nijeriya

A cikin wata sanarwa da aka fitar, shugaban sashen yada labarai da wayar da kan jama’a na EFCC, Dele Oyewale, ya bayyana cewa Otukpa ya yi amfani da lakabi da dama, da suka hada da Ford Thompson, Oscar Donald Tyler, Michael Haye, Jose Bitto, da Kristin Dabidson, domin aiwatar da wannan zamba.

Ayyukan damfara sun ta’allaka ne a kan wani dan damfara na cryptocurrency mai suna Likuid Asset Group, wanda Otukpa ya habaka sosai a kafafen sada zumunta. An kwadaitar da wadanda aka damfara zuwa saka hannun jari a dandalin, wanda ya haifar da hasarar kudi mai yawa.

Hukumar EFCC ta bayyana cewa an shigar da kudaden da aka samu daga wannan badakalar zuwa asusun bankin Otukpa ta hanyar dandalin musayar cryptocurrency na duniya.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Sanarwar ta ce: “Hukumomin EFCC sun kama wani da ake zargi da damfara ta intanet, Osang Usie Otukpa, bisa zargin damfarar wasu ‘yan kasar Australia 139 da suka kai Dalar Amurka 8,000,000.

“An kama shi ne a filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Mohammed, Ikeja, Legas, bayan isowarsa daga kasar Amurka a ranar Juma’a 6 ga watan Disamba, 2024.

“Otukpa, wanda yake da synaye biyar da suka hada da-Ford Thompson, Oscar Donald Tyler, Michael Haye, Jose Bitto, da Kristin Dabidson – ya zambaci mutanen ta hanyar jawo su a kan kafofin yada labarun don saka hannun jari a dandalin sa hannun jari na cryptocurrency, Likuid Asset Group.

“An karkatar da kudaden zuwa asusun ajiyarsa ta hanyar dandalin musayar cryptocurrency na duniya.”

Oyewale ya ci gaba da cewa, ana ci gaba da gudanar da bincike, kuma za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala aikin. Wannan ci gaban ya bayyana kokarin da EFCC ke yi na murkushe masu aikata laifuka ta intanet da kuma dawo da amana ga tsarin hada-hadar kudi a duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Auren Bogi: An Garkame Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Zambar Fiye Da Naira Miliyan 9

Next Post

Bangarorin Da Suka Fi Samun Kaso Mai Tsoka A Kasafin Kudin 2025

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

59 minutes ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

2 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

4 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

7 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

9 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

10 hours ago
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tsawaita Kasafin 2024 Zuwa Watanni 6 – Akpabio

Bangarorin Da Suka Fi Samun Kaso Mai Tsoka A Kasafin Kudin 2025

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.