ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bangarorin Da Suka Fi Samun Kaso Mai Tsoka A Kasafin Kudin 2025

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
Kasafin Kudin 2025

A ranar Laraba ce, Shugaban kasa Bola Tinubu ya gurfana a zauren hadakar majalisun tarayya guda biyu domin gabatar da kudirin kasafin kudin 2025 na naira triliyan 47.9.

Akwai muhimman bangarori da suka fi samun kaso mai tsoka a cikin kasafin kudin na 2025. Inda bangaren tsaro ya yi zarra da naira triliyan 4.91.

  • Yahaya Bello Ya Samu Beli Bayan Cika Sharudan Kotu
  • Majalisar Wakilai Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Wa Hukumar NEPC Kudaden Aiki

Sannan bangarorin kayayyakin more rayuwa, Lafiya, da Ilimi za suka samu naira tiriliyan 4.06, naira tiriliyan 2.48 da kuma naira tiriliyan 3.5, bi da bi.

ADVERTISEMENT

Kudirin kasafin kudin mai taken, “Kudirin kasafin kudi na maidowa da tabbatar da zaman lafiya da samun nasara.”

Tinubu ya bayyana cewa, “Babban abin da ke cikin kasafin kudin 2025, bangaren tsaro ya samu naira tiriliyan 4.91, bangaren samar da ababen more rayuwa ya samu naira tiriliyan 4.06, bangaren lafiya ya samu naira tiriliyan 2.48, sannan kuma bangaren ilimi ya samu naira tiriliyan 3.5.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Yayin da muka fara aiwatar da kasafin kudin shekarar 2025, za mu dauki matakan na ba sani, ba sabo, mun yanke shawarar musu muhimmanci, kuma abubuwan da muka sa a gaba a bayyane suke. Wannan kasafin kudin yana nuna sabon alkawari na karfafa tushen tattalin arziki mai karfi.

“A duk lokacin da muke gyara muhimman sassa masu mahimmanci domin samun ci gaba, muna sa ran tabbatar da tsaron kasarmu. Tsaro shi ne ginshikin duk wani ci gaba. Mun kara wa sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro kudade sosai don tabbatar da tsaron kasa da kare iyakokinmu da kuma karfafa ikon gwamnati a kan kowane farfajiyar kasarmu.”

Tinubu ya tabbatar da cewa, “Gwamnati za ta ci gaba da bai wa jami’an tsaro kayayyakin aiki na zamani da na’urorin zamani da suke bukata domin kare lafiyar al’umma, da inganta tarbiyyar maza da mata a cikin rundunar soji shi ne babban abin da gwamnatinmu ta sa a gaba, manyan jami’an tsaro maza da mata na sojojinmu da na ‘yansandan Nijeriya za su kare al’ummarmu, gwamnatinmu za ta ci gaba da ba su karfin gwiwa domin murkushe ‘yan ta’adda, ‘yan fashi da kuma masu barazana ga ’yancin kanmu.”

Da yake jawabi kan kasafin kudin, Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana cewa za a tsawaita tsawon lokacin kasafin kudin shekarar 2024 zuwa ranar 25 ga watan Yunin 2025.

Ya bayyana haka ne cikin jawabinsa na bude taron gabatar da kasafin 2025 da Shugaba Tinubu ya yi a zauren hadakar majalisun tarayya wanda ya kunshi majalisar dattawa da ta wakilai.

A cewarsa, kaso 50 ne na kasafin kudin shekarar 2024 ya aiwatu, inda ya bar gibin kaso 50 da ba a aiwatar ba, don haka, akwai bukatar tsawaita lokaci don aiwatar da shi yadda ya dace.

Kasafin Kudin 2025
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Kasafin Kudin 2025
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Ba Mijina Ba Ne Sanadin Ƙuncin Rayuwa Da Ake Ciki A Nijeriya – Uwargidan Shugaban Ƙasa

Uwargidan Shugaban Kasa Ta Yi Rabon Tallafi Ga Tsofaffi A Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.