ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bangarorin Da Suka Fi Samun Kaso Mai Tsoka A Kasafin Kudin 2025

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
Kasafin Kudin 2025

A ranar Laraba ce, Shugaban kasa Bola Tinubu ya gurfana a zauren hadakar majalisun tarayya guda biyu domin gabatar da kudirin kasafin kudin 2025 na naira triliyan 47.9.

Akwai muhimman bangarori da suka fi samun kaso mai tsoka a cikin kasafin kudin na 2025. Inda bangaren tsaro ya yi zarra da naira triliyan 4.91.

  • Yahaya Bello Ya Samu Beli Bayan Cika Sharudan Kotu
  • Majalisar Wakilai Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Wa Hukumar NEPC Kudaden Aiki

Sannan bangarorin kayayyakin more rayuwa, Lafiya, da Ilimi za suka samu naira tiriliyan 4.06, naira tiriliyan 2.48 da kuma naira tiriliyan 3.5, bi da bi.

ADVERTISEMENT

Kudirin kasafin kudin mai taken, “Kudirin kasafin kudi na maidowa da tabbatar da zaman lafiya da samun nasara.”

Tinubu ya bayyana cewa, “Babban abin da ke cikin kasafin kudin 2025, bangaren tsaro ya samu naira tiriliyan 4.91, bangaren samar da ababen more rayuwa ya samu naira tiriliyan 4.06, bangaren lafiya ya samu naira tiriliyan 2.48, sannan kuma bangaren ilimi ya samu naira tiriliyan 3.5.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

“Yayin da muka fara aiwatar da kasafin kudin shekarar 2025, za mu dauki matakan na ba sani, ba sabo, mun yanke shawarar musu muhimmanci, kuma abubuwan da muka sa a gaba a bayyane suke. Wannan kasafin kudin yana nuna sabon alkawari na karfafa tushen tattalin arziki mai karfi.

“A duk lokacin da muke gyara muhimman sassa masu mahimmanci domin samun ci gaba, muna sa ran tabbatar da tsaron kasarmu. Tsaro shi ne ginshikin duk wani ci gaba. Mun kara wa sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro kudade sosai don tabbatar da tsaron kasa da kare iyakokinmu da kuma karfafa ikon gwamnati a kan kowane farfajiyar kasarmu.”

Tinubu ya tabbatar da cewa, “Gwamnati za ta ci gaba da bai wa jami’an tsaro kayayyakin aiki na zamani da na’urorin zamani da suke bukata domin kare lafiyar al’umma, da inganta tarbiyyar maza da mata a cikin rundunar soji shi ne babban abin da gwamnatinmu ta sa a gaba, manyan jami’an tsaro maza da mata na sojojinmu da na ‘yansandan Nijeriya za su kare al’ummarmu, gwamnatinmu za ta ci gaba da ba su karfin gwiwa domin murkushe ‘yan ta’adda, ‘yan fashi da kuma masu barazana ga ’yancin kanmu.”

Da yake jawabi kan kasafin kudin, Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana cewa za a tsawaita tsawon lokacin kasafin kudin shekarar 2024 zuwa ranar 25 ga watan Yunin 2025.

Ya bayyana haka ne cikin jawabinsa na bude taron gabatar da kasafin 2025 da Shugaba Tinubu ya yi a zauren hadakar majalisun tarayya wanda ya kunshi majalisar dattawa da ta wakilai.

A cewarsa, kaso 50 ne na kasafin kudin shekarar 2024 ya aiwatu, inda ya bar gibin kaso 50 da ba a aiwatar ba, don haka, akwai bukatar tsawaita lokaci don aiwatar da shi yadda ya dace.

Kasafin Kudin 2025
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Kasafin Kudin 2025
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
Ba Mijina Ba Ne Sanadin Ƙuncin Rayuwa Da Ake Ciki A Nijeriya – Uwargidan Shugaban Ƙasa

Uwargidan Shugaban Kasa Ta Yi Rabon Tallafi Ga Tsofaffi A Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.