ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bangarorin Da Suka Fi Samun Kaso Mai Tsoka A Kasafin Kudin 2025

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
Kasafin Kudin 2025

A ranar Laraba ce, Shugaban kasa Bola Tinubu ya gurfana a zauren hadakar majalisun tarayya guda biyu domin gabatar da kudirin kasafin kudin 2025 na naira triliyan 47.9.

Akwai muhimman bangarori da suka fi samun kaso mai tsoka a cikin kasafin kudin na 2025. Inda bangaren tsaro ya yi zarra da naira triliyan 4.91.

  • Yahaya Bello Ya Samu Beli Bayan Cika Sharudan Kotu
  • Majalisar Wakilai Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Wa Hukumar NEPC Kudaden Aiki

Sannan bangarorin kayayyakin more rayuwa, Lafiya, da Ilimi za suka samu naira tiriliyan 4.06, naira tiriliyan 2.48 da kuma naira tiriliyan 3.5, bi da bi.

ADVERTISEMENT

Kudirin kasafin kudin mai taken, “Kudirin kasafin kudi na maidowa da tabbatar da zaman lafiya da samun nasara.”

Tinubu ya bayyana cewa, “Babban abin da ke cikin kasafin kudin 2025, bangaren tsaro ya samu naira tiriliyan 4.91, bangaren samar da ababen more rayuwa ya samu naira tiriliyan 4.06, bangaren lafiya ya samu naira tiriliyan 2.48, sannan kuma bangaren ilimi ya samu naira tiriliyan 3.5.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Yayin da muka fara aiwatar da kasafin kudin shekarar 2025, za mu dauki matakan na ba sani, ba sabo, mun yanke shawarar musu muhimmanci, kuma abubuwan da muka sa a gaba a bayyane suke. Wannan kasafin kudin yana nuna sabon alkawari na karfafa tushen tattalin arziki mai karfi.

“A duk lokacin da muke gyara muhimman sassa masu mahimmanci domin samun ci gaba, muna sa ran tabbatar da tsaron kasarmu. Tsaro shi ne ginshikin duk wani ci gaba. Mun kara wa sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro kudade sosai don tabbatar da tsaron kasa da kare iyakokinmu da kuma karfafa ikon gwamnati a kan kowane farfajiyar kasarmu.”

Tinubu ya tabbatar da cewa, “Gwamnati za ta ci gaba da bai wa jami’an tsaro kayayyakin aiki na zamani da na’urorin zamani da suke bukata domin kare lafiyar al’umma, da inganta tarbiyyar maza da mata a cikin rundunar soji shi ne babban abin da gwamnatinmu ta sa a gaba, manyan jami’an tsaro maza da mata na sojojinmu da na ‘yansandan Nijeriya za su kare al’ummarmu, gwamnatinmu za ta ci gaba da ba su karfin gwiwa domin murkushe ‘yan ta’adda, ‘yan fashi da kuma masu barazana ga ’yancin kanmu.”

Da yake jawabi kan kasafin kudin, Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana cewa za a tsawaita tsawon lokacin kasafin kudin shekarar 2024 zuwa ranar 25 ga watan Yunin 2025.

Ya bayyana haka ne cikin jawabinsa na bude taron gabatar da kasafin 2025 da Shugaba Tinubu ya yi a zauren hadakar majalisun tarayya wanda ya kunshi majalisar dattawa da ta wakilai.

A cewarsa, kaso 50 ne na kasafin kudin shekarar 2024 ya aiwatu, inda ya bar gibin kaso 50 da ba a aiwatar ba, don haka, akwai bukatar tsawaita lokaci don aiwatar da shi yadda ya dace.

Kasafin Kudin 2025
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
Kasafin Kudin 2025
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Ba Mijina Ba Ne Sanadin Ƙuncin Rayuwa Da Ake Ciki A Nijeriya – Uwargidan Shugaban Ƙasa

Uwargidan Shugaban Kasa Ta Yi Rabon Tallafi Ga Tsofaffi A Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.