• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bangarorin Da Suka Fi Samun Kaso Mai Tsoka A Kasafin Kudin 2025

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tsawaita Kasafin 2024 Zuwa Watanni 6 – Akpabio
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Laraba ce, Shugaban kasa Bola Tinubu ya gurfana a zauren hadakar majalisun tarayya guda biyu domin gabatar da kudirin kasafin kudin 2025 na naira triliyan 47.9.

Akwai muhimman bangarori da suka fi samun kaso mai tsoka a cikin kasafin kudin na 2025. Inda bangaren tsaro ya yi zarra da naira triliyan 4.91.

  • Yahaya Bello Ya Samu Beli Bayan Cika Sharudan Kotu
  • Majalisar Wakilai Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Wa Hukumar NEPC Kudaden Aiki

Sannan bangarorin kayayyakin more rayuwa, Lafiya, da Ilimi za suka samu naira tiriliyan 4.06, naira tiriliyan 2.48 da kuma naira tiriliyan 3.5, bi da bi.

Kudirin kasafin kudin mai taken, “Kudirin kasafin kudi na maidowa da tabbatar da zaman lafiya da samun nasara.”

Tinubu ya bayyana cewa, “Babban abin da ke cikin kasafin kudin 2025, bangaren tsaro ya samu naira tiriliyan 4.91, bangaren samar da ababen more rayuwa ya samu naira tiriliyan 4.06, bangaren lafiya ya samu naira tiriliyan 2.48, sannan kuma bangaren ilimi ya samu naira tiriliyan 3.5.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

“Yayin da muka fara aiwatar da kasafin kudin shekarar 2025, za mu dauki matakan na ba sani, ba sabo, mun yanke shawarar musu muhimmanci, kuma abubuwan da muka sa a gaba a bayyane suke. Wannan kasafin kudin yana nuna sabon alkawari na karfafa tushen tattalin arziki mai karfi.

“A duk lokacin da muke gyara muhimman sassa masu mahimmanci domin samun ci gaba, muna sa ran tabbatar da tsaron kasarmu. Tsaro shi ne ginshikin duk wani ci gaba. Mun kara wa sojoji da ‘yansanda da sauran jami’an tsaro kudade sosai don tabbatar da tsaron kasa da kare iyakokinmu da kuma karfafa ikon gwamnati a kan kowane farfajiyar kasarmu.”

Tinubu ya tabbatar da cewa, “Gwamnati za ta ci gaba da bai wa jami’an tsaro kayayyakin aiki na zamani da na’urorin zamani da suke bukata domin kare lafiyar al’umma, da inganta tarbiyyar maza da mata a cikin rundunar soji shi ne babban abin da gwamnatinmu ta sa a gaba, manyan jami’an tsaro maza da mata na sojojinmu da na ‘yansandan Nijeriya za su kare al’ummarmu, gwamnatinmu za ta ci gaba da ba su karfin gwiwa domin murkushe ‘yan ta’adda, ‘yan fashi da kuma masu barazana ga ’yancin kanmu.”

Da yake jawabi kan kasafin kudin, Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana cewa za a tsawaita tsawon lokacin kasafin kudin shekarar 2024 zuwa ranar 25 ga watan Yunin 2025.

Ya bayyana haka ne cikin jawabinsa na bude taron gabatar da kasafin 2025 da Shugaba Tinubu ya yi a zauren hadakar majalisun tarayya wanda ya kunshi majalisar dattawa da ta wakilai.

A cewarsa, kaso 50 ne na kasafin kudin shekarar 2024 ya aiwatu, inda ya bar gibin kaso 50 da ba a aiwatar ba, don haka, akwai bukatar tsawaita lokaci don aiwatar da shi yadda ya dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kudin Kirifto: An Cafke Dan Nijeriya Da Laifin Damfarar ‘Yan Australiya Dala Miliyan 8

Next Post

Uwargidan Shugaban Kasa Ta Yi Rabon Tallafi Ga Tsofaffi A Jihar Kogi

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

4 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

5 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

7 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

10 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

12 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

13 hours ago
Next Post
Ba Mijina Ba Ne Sanadin Ƙuncin Rayuwa Da Ake Ciki A Nijeriya – Uwargidan Shugaban Ƙasa

Uwargidan Shugaban Kasa Ta Yi Rabon Tallafi Ga Tsofaffi A Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.