• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
10 months ago
Mata

Zahra’u Adam Matashiya ce mai hazaka da jajircewa kan neman ilimi, inda ta shawarci mata da su dage da karatu domin a cewarta idan mata suka yi karatu za su taimakawa kansu da ‘ya’yansu, baya ga haka ta bayyana wa wakiliyarmu BILKISU TIJJANI KASSIM, irin nasarori da kalubalen da ta fuskanta, kamar dai yadda za ku karanta kamar haka:

 

Da farko za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

Sunana Zara’u Adamu Sulaiman, an haife ni a garin Hadejia, na yi primary da sikandire a Usman bin Affan, kuma na yi sikandire a GGDSS Hadejia yanzu ina NCE a College Of Education Legel Studies.

 

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Zara’u kina da aure ce?

A a bani da aure

 

Malama Zara’u kina da wata sana’a ne ko kuma karatun aka sa gaba?

A’a gaskiya kasancewar ni daliba ce, gaskiya ni ba ni da wata sana’a, sai dai karatu, shi na sa a gaba, tukunnan sana’a, sai mun kammala karatu in sha Allahu.

 

Me kike karanta?

Ina karantar fannin Tattalin Arziki da Turanci

 

Me yaja hankalinki da har kike sha’awar wannan karatun wadannan fannoni?

Saboda ina da sha’awar sanin harkokin kasa ciki da waje, sannan in san yadda ake tattalin arzikin kasa da na gida musamman ma ina ganin ni mace ce da zan rike gida.

Idan na iya tattala kayan gida, na iya adana su ba’a almabozarancin su, to ina ganin wannan ma yana da kyau.

Sannan idan na karanci tattali zan san abubuwan da suka shafi kasa, abubuwan da ya kama a yi a kasa da wanda bai kamata ba. Za ka gane yadda ake lafiyar da kasar ya yi daidai ko bai yi ba.

 

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin karatunki?

Zngon karatuna na biyu, a matakin karatuna na uku na fiuskanci kalubale da dama, wanda sai dai na yi addau’a da fatan kada na sake samun irin wannan abin, Allah ya kiyaye mana gaba.

 

Zuwa yanzu wadanne irin nasarori kika samu?

To Alhamdulillah ka ga komai naka yana tafiya yadda ya kamata, karatun na babu wata matsala, to wannan ba karamar nasara bace a wajena, gashi yanzu har mun kawo shekara ta karshe, muna zango na karshe kwanaki kadai ya rage mu kammala ai sai dai na ce Alhamdulillah.

 

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da karatunki?

Abin da yafi faranta min rai game da karatuna, shi ne na shiga jarabawa na ga na gane kowace tambaya, a gasukiya wannan ba karamin jin dadi nake ba, yana farantamin rai sosai.

 

Dame kike so mutane su rika tunawa dake?

Ina so mutane su rinka tunawa da ni akan hakuri na da son zaman Lafiya.

 

Wanne irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

A ce Allah ya yi min albarka ya kuma jikan mahaifana a gaskiya ina jin dadin wannan addu’ar sosai kuma tana birge ni.

 

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Ina samun goyon baya daga wajen iyaye na sosai da sosai, saboda su ke karfafa min gwiwa wajen na jajirce akan karatu na, kuma su suka saka ni a makaranta tun ina karama har na kawo yanzu, to babu abin da zan ce da su sai godiya, ina gode wa Allah Alhamdulillah, sannan ina gode wa iyayena sosai.

 

Kawaye fa?

Kawata daya ce mai suna zaliha, muna tare da ita muna karatu.

 

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Cikin kayan sawa ina son dogowar riga ta yadi, kayan kwalliya kuma gaskiya ni ba ma’abociyar kwalliya bace.

 

A karshe wanne irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Shawarata a gareku ‘yan uwana mata ku dage da karatu domin tallafawa rayuwarku da ta ‘ya’yanku

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

August 31, 2025
Next Post
Babban Aikin “Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana A Wajen Da Ake Kiwon Kifi” A Sin Ya Fara Aiki

Babban Aikin “Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana A Wajen Da Ake Kiwon Kifi” A Sin Ya Fara Aiki

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.