• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana’antar Kannywood Ta Sauka Daga Kan Turbar Da Tun Farko Aka Ginata -Tahir Fagge 

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
8 months ago
in Nishadi
0
Masana’antar Kannywood Ta Sauka Daga Kan Turbar Da Tun Farko Aka Ginata -Tahir Fagge 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin wadanda aka assasa babbar masana’antar nishadi da ke amfani da harshen Hausa wajen isar da sako a fadin Duniya wadda ake wa lakabi da Kannywood kuma ta ke da matsugini a babban birni mai tarihi wato Kano,Tahir Fagge ya ce masana’antar a yanzu ta sauka daga kan turbar da tun farko aka gina ta akai.

Jarumin a wata hira da ya yi ya ce tun farko an gina masana’antar a kan wasu manyan tubali da suka hada da kaunar juna, shawarwari da kuma shugabanci nagari, amma yanzu an rasa wasu daga cikinsu saboda zuwan zamani da sauran dalilai.

  • Ban Hadu Da Wani Kalubale A Lokacin Shiga Masana’antar Kannywood Ba -Fiddausi Yahaya
  • Matsalar Tsaro: Matawalle Ya Ziyarci Jihar Zamfara

Tahir ya ce a baya duk wani dan Kannywood ya na matukar ganin dan uwansa ya samu karuwa idan kuma wata matsala ta faru dashi, zai jajanta mashi sannan idan akwai wani taimako da zai iya yi wajen fitar wannan damuwar zai yi ba kamar yanzu da kowa kanshi ya sani ba.

A zamanin baya idan wani zai shirya fim zai kawo labarin fim din a gaban manya a cikin masana’antar sai a duba a gani idan akwai wani gyara a yi idan kuma babu gyara sai a bashi shawarwarin da suka dace, sannan a baya akwai zumunci mai karfi a tsakanin wadanda ke cikin masana’antar, amma zuwan wayoyin hannu ya sa sai dai mutum ya kiraka a waya ya yi maka murna ko ya jajanta maka ba tare da ya zo har inda kake ba inji shi.

Dangane da shigowar manhajar YouTube da sauran shafukan yanar gizo inda ake dora fina finai a maimakon faifan cd da ake yi lokacin baya, Fagge ya kira wannan abu da ci gaban mai hakar rijiya domin kuwa ya na yin kasa ya na cewa an samu ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Idan kuka lura a baya mutum ya kan cire kudmdi kalilan ya yi fim dinsa mai kyau ya tafi kasuwa ya sayar ya samu riba mai yawa ba tare da wata tangarda ba, amma yanzu sai ka zuba makudan kudade wajen neman mabiya a shafukan yanar gizo wadanda za su dinga kallon fina finanka da kake dorawa lokaci bayan lokaci sannan ne za ka samu wani abin kirki.

Da aka tabo batun yadda wani lokaci a baya aka gane shi a wani waje wanda ake kyautata zaton gidan rawa ne kokuma gidan solo kamar yadda wasu suka sani, kuma har ta kai ga wadansu na ganin bai dace babban mutum kamar shi ya tafi irin wadannan wuraren da aka sani mafi yawancin wadanda ke wajen matasa ne da suka tafi domin a nishadantar dasu ba.

Tahir Fagge ya ce zuwa gidan solon da aka gani ya je ba haka kawai ya tafi ba, domin kuwa an iske shi har gida aka nemi ya tafi a matsayin babban bako a wurin wanda a wancan lokacin yake sabon budewa, bayan ya tafi ne kuma suka bukaci ya nishadantar da wadanda ke wajen kuma a matsayinsa na jarumi kuma wanda yake da masoya sai ya ga idan yaki ba za su ji dadi ba.

Bayan an saka wata wakar da a wajen aka rasa wanda zai iya taka rawar ta, duba da cewa tsohuwar waka ce sai ya yi zumbur ya tashi ya taka rawa domin ya nunawa matasan da ke wajen cewa da tsohuwar zuma ake magani, hakan ya sa mahukuntan wajen su ka ji dadi har suka yi mashi kyautar manyan kudade wanda a wannan lokacin yake da matukar bukatar kudi domin tafiya neman magani in ji shi.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Me Ke Kawo Yawan Tashin Gobara A Wannan Lokaci Na Hunturu?

Next Post

Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

Related

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
Nishadi

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

8 hours ago
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Nishadi

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

7 days ago
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami
Nishadi

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

7 days ago
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa
Nishadi

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

2 weeks ago
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Nishadi

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

4 weeks ago
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

1 month ago
Next Post
Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.