• English
  • Business News
Tuesday, June 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Karɓi Bashin Dala Biliyan 1.5 Daga Bankin Duniya Bayan Cire Tallafin Mai

by Khalid Idris Doya
5 months ago
in Manyan Labarai
0
Nijeriya Ta Karɓi Bashin Dala Biliyan 1.5 Daga Bankin Duniya Bayan Cire Tallafin Mai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bankin Duniya ta mika dala biliyan 1.5 a matsayin rancen waje ga Nijeriya a cikin yunkurin gwamnatin tarayya na aiwatar da cire tallafin man fetur da kuma yin kwaskwarima ga dokar haraji.

Wannan na kunshe ne a bayanin rancen da Bankin Duniyar ya fitar a baya-bayan nan.

Rancen wanda zai taimaka wajen farfado da tattalin arziki da aiwatar da manufofin kyautata harkokin kudi a cikin watanni shida.

  • Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa
  • Bayan Cire Tallafin Mai Da Gyaran Dokar Haraji, Bankin Duniya Ya Danƙa Wa Nijeriya Bashi

Bayanin bankin ya nuna cewa an amince da bashin ne a ranar 3 ga watan Yunin 2024, kuma an sake kason farko na dala miliyan 750 a ranar 2 ga watan Yulin 2024, yayin da kuma aka turo wa Nijeriya sauran kudin a watan Disamba.

Kudin na dala biliyan 1.5 an bai wa Nijeriya da tsarin biya a lokuta daban-daban da nufin taimakawa wajen gudanar da ayyukan da za su farfado da tattalin arziki.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

Rancen farko na dala miliyan 750 da aka samu daga kungiyar ci gaban kasa da kasa na da tsawon shekaru 12 domin a biya. Yayin da kuma rance na biyun wato na dala miliyan 750 shi kuma za a biya shi a cikin shekaru 24 masu zuwa.

A cewar Bankin Duniyan, rancen da ta bai wa Nijeriya za ta taimaka wajen aiwatar da manufofin da za su kai ga farfadowa daga cire tallafin mai da daidaita musayar canjin kudi da kuma manufofin haraji.

Idan za a tuna dai a watan Oktoban 2024, gwamnatin tarayya ta mika kudirin gyara dokar haraji ga majalisar dokoki na kasa domin neman amincewa, wanda dokar ta janyo cece-kuce a tsakanin ‘yan Nijeriya, musamman shugabannin Arewa da suke zargin dokar ka iya janyo musu nakasu.

“An kuma aiwatar da garambawul don daidaita kasuwar man fetur gabaki daya, tare da tabbatar da cewa an kayyade farashin kayayyaki bisa yanayin kasuwa da bude fannin gasa. Hukumomin suna bin diddigin alkawarin da suka yi na dakatar da kasafin kudi tare da dogaro da daidaitattun kayan bashi don samar da givin.”

A halin da ake ciki, a cikin watannin da suka gabata, tsarin tagwayen manufofin gwamnati na cire da tallafin man fetur da hadewar musayar kudade ya jawo yabo, yayin da wasu kuma suka yi ta yir da su.

Musamman, a karkashin manufofin, farashin man fetur ya karu sau biyar, kuma farashin canji ya karu, wanda ya janyo tsadar rayuwa ga yawancin ‘yan Nijeriya.

Ko da yake gwamnatin tarayya ta vullo da hanyoyin yayyafa ruwa ga matsalar, kamar bayar da naira 25,000 ga gidaje, wanda gidaje miliyan biyu suka amfana, aiwatar da shirin amfani da motoci masu amfani da iskar gas, wanda shi ne mafi arha a kan mai don rage tasirin cire tallafin mai.

Lamarin ya janyo har tasirin hauhawar farashin kayan abinci, ya haura zuwa kashi 34.60 da kashi 39.93, bi da bi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Banki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Jaddada Aniyarta Ta Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Yammacin Afirka

Next Post

ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

Related

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu
Manyan Labarai

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

2 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

5 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

9 hours ago
Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran
Kasashen Ketare

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

10 hours ago
Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna
Manyan Labarai

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

12 hours ago
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

15 hours ago
Next Post
ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

June 17, 2025
Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

June 17, 2025
Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

June 17, 2025
An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

June 17, 2025
Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

June 17, 2025
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

June 17, 2025
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

June 17, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

June 17, 2025
Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

June 17, 2025
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

June 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.