• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzon Gwamnan 2024 – Alhaji Abba Kabir Yusuf

by Leadership Hausa
7 months ago
in Labarai, Siyasa
0
Gwarzon Gwamnan 2024  – Alhaji Abba Kabir Yusuf
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya samu lambar yabo ta Gwarzon Gwamnan Shekarar 2024 ta Jaridar LEADERSHIP, saboda gagarumin aikin da ya yi a fannin ilimi da sauran muhimman bangarorin ci gaba a Jihar Kano

Gwamnatinsa ta ayyana dokar ta-baci kan ilimi tare da ware kashi 31 na kasafin kudin jihar na Naira biliyan 570, kwatankwacin Naira biliyan 165.4, a bangaren ilimi. Wannan matakin na nufin magance matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta, wadda Kano ce ke kan gaba na mafi yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya, da kuma bai wa yara marasa galihu damar samun ingantaccen ilimi.

  • Dokar Haraji Za Ta Ƙara Jefa Al’umma Cikin Talauci – Gwamnatin Kano
  • Dubun Wata Budurwa Da Wasu 5 Ya Cika Bayan Ta Sace Wayoyin Salula 30 Na Matan Aure A Kano

Gwamna Yusuf ya yi sabbin gine-gine a makarantu, ya samar da kujeru da tebura da sauran kayan karatu. Haka kuma, gwamnatinsa ta bayar da tallafin karatu ga matasa maza da mata da yawa don yin karatu a kasashen waje, don tabbatar da cewa ilimi ya zama ginshikin ci gaban jihar.

Shahararsa da kalaman “ilimi, ilimi, ilimi” sun tabbatar da cewa bangaren ilimi shi ne abin da ya fi bai wa fifiko.

An haifi Alhaji Abba Kabir Yusuf a gidan Sarautar Fulanin Sullubawa, wanda suke wani tsagi ne daga sarakunan Masarautar Kano. Ya yi kuruciyarsa a Gaya, a hannun kakansa, Alhaji Yusuf Bashari, Hakimin Gaya. Ya yi karatunsa na Firamare da Sakandire a Kano kafin samun difiloma a Fannin Injiniyan Ruwa da Muhalli a Kwalejin Fasaha ta Mubi da Kaduna Polytechnic.

Labarai Masu Nasaba

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

Daga baya, Gwamna Yusuf ya samu shaidar digiri a fannin gudanarwa a Jami’ar Bayero ta Kano. Abba Kabir Yusuf ya fara aikinsa a Hukumar Ruwa ta Jihar Kano, inda ya samu gogewa a fannin aikin gwamnati. Har ila yau, ya taba rike mukamin shugaban kwamitin gudanarwa na Cibiyar Shirye-shiryen Ilimi da Gudanarwa ta kasa.

A siyasance, Abba Kabir Yusuf ya fara aikinsa a karkashin jagorancin tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, inda ya rike mukamai daban-daban, ciki har da mataimaki na musamman da mukamin sakatare na musamman da mukamin babban sakatare, da kuma Kwamishinan ayyuka, gidaje da sufuri na Jihar Kano.

A shekarar 2018, ya tsaya takarar gwamna karkashin jam’iyyar PDP, wanda daga nan ne ma ya samo lakabin sunan “Abba Gida-gida.” Duk da cewa bai yi nasara ba a wancan lokacin, amma bai karaya ba. A shekarar 2023, ya sauya sheka zuwa jam’iyyar NNPP tare da Jagoransa Sanata Kwankwaso, kuma ya lashe zaben gwamnan jihar.

Bayan lashe zaben, Abba Kabir Yusuf ya fuskanci kalubale na siyasa, ciki har da soke zabensa a kotun sauraron kararrakin zabe. Sai dai, ya daukaka kara zuwa Kotun Koli, inda aka tabbatar da zabensa a matsayin gwamnan jihar a watan Janairu 2024. Wannan karfin hali da juriya da ya nuna sun kara masa daraja a matsayin shugaba wanda ba ya barin wani abu ya shagaltar da shi daga kokarin ciyar da jiharsa ta Kano gaba.

A wajen inganta rayuwar al’ummar Kano kuwa, Gwamna Yusuf yana gina sabbin gadoji a Kofar Dan Agundi da Tal’udu, domin rage cinkoson ababen hawa a jihar. Haka kuma, ya inganta fannin kiwon lafiya ta hanyar samar da kayan aiki da magunguna a asibitoci kyauta. Gwamnatinsa ta kuma kaddamar da shirin tallafa wa mata 5,200 da kudi Naira 50,000 a matsayin jari. Wannan tallafi na nufin taimaka wa mata wajen karfafa wa kasuwancinsu da rage talauci a tsakaninsu.

Haka kuma, gwamnatinsa ta canza fitilun kan titunan Kano zuwa masu amfani da hasken rana, wanda ya sanya titunan jihar zama cikin haske ko yaushe tare da rage amfani da makamashi mara tsafta. Gwamna Yusuf yana biyan albashi, fansho, da kudin sallama akai-akai, kuma ya kasance cikin gwamnonin farko a Nijeriya da suka fara aiwatarwa da biyan mafi karancin albashi na Naira 71,000. Bugu da kari, gwamnatinsa ta biya bashin Naira biliyan 3.5 na kasashen waje da Naira biliyan 60 na cikin gida, ta rage bashin jihar zuwa Naira biliyan 127.8 a tsakiyar shekarar 2024.

Alhaji Abba Kabir Yusuf ya zama jajirtaccen gwamna wanda ya yi fice wajen kawo sauyi a fannin ilimi da lafiya da gine-gine da kuma tallafa wa jama’a. Jagorancinsa ya zama abin misali a Nijeriya, burinsa bai wuce sanya murmushi a fuskar Kanawa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: kano
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Damfari ‘Yan Nijeriya Naira Biliyan 93.72 A Shekaru 2 – Bincike

Next Post

Nijeriya Ta Jaddada Aniyarta Ta Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Yammacin Afirka

Related

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
Labarai

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

39 minutes ago
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027
Siyasa

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

2 hours ago
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
Tsaro

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

4 hours ago
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
Manyan Labarai

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

5 hours ago
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

6 hours ago
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
Manyan Labarai

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

7 hours ago
Next Post

Nijeriya Ta Jaddada Aniyarta Ta Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Yammacin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

August 10, 2025
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.