• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai

...Ta Nemi Karin Kasafin Kuɗi Ga Ma’aikatar yada labarai da wayar da kai

by Sulaiman
10 months ago
Minista

Majalisar Dattawa ta yaba wa Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, bisa ƙoƙarinsa wajen gudanarwa da yaɗa bayanai kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati.  

 

An yi masa wannan yabon ne a ranar Talata yayin da ya bayyana a gaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Yaɗa Labarai don kare kasafin kuɗin ma’aikatarsa na shekarar 2025.

  • Arsenal Ta Matsawa Liverpool Ƙaimi Bayan Doke Tottenham A Emirates 
  • Karkashin BRI Sin Ta Yi Hadin Gwiwar Samar Da Dakunan Gwaje-gwaje Sama Da 70

Sanatocin sun jinjina wa ƙoƙarin ma’aikatar amma sun nuna damuwa kan ƙarancin kuɗaɗen da aka ware mata, suna masu cewa ba zai wadatar ba don aiwatar da aikin ta na yaɗa labarai kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati.

 

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

Sun buƙaci a samar da ƙarin kasafin kuɗi na musamman domin a ƙarfafa wa ma’aikatar gwiwa.

 

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan (PDP-Kogi) ta jaddada bambancin kasafin kuɗin ma’aikatar da na ƙasar Afirka ta Kudu, inda ta bayyana cewa Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Afirka ta Kudu ta samu kimanin naira biliyan 409 don aiwatar da shirye-shiryen ta.

 

Ta ce Nijeriya, wadda ke da yawan al’umma fiye da waccan ƙasar, ya kamata ta ware ƙarin kuɗi don shirye-shiryen ta na yaɗa labarai.

 

Ta kuma jaddada muhimmancin wayar da kan al’umma, musamman matasa, da kuma yadda ministan da tawagar sa suke shirye don aiwatar da hakan idan aka ƙara masu kuɗi.

 

Shi kuwa Sanata Abdul Ningi (PDP-Bauchi) ya yaba wa ministan bisa ƙwarewar sa, jagorancin sa, da kuma cigaban da aka samu a hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar, musamman ta fuskar cigaba da aka samu a Hukumar Tlabijin ta Nijeriya (NTA).

 

A nasa jawabin, Shugaban Kwamitin, Sanata Ken Eze (APC-Ebonyi), ya buƙaci ma’aikatar da ta ƙirƙiro hanyoyin samun kuɗaɗen shiga.

 

Ya kuma buƙaci a sake duba kasafin kuɗin, yana mai jaddada muhimmancin ɓangaren yaɗa labarai ga nasarar gwamnati.

 

Ya ce: “Ba za a iya yin abubuwa da yawa ba idan babu kuɗaɗen shiga, kuma bayanai suna da matuƙar muhimmanci: muna buƙatar ɓangaren ya jagoranci manufofi da shirye-shiryen gwamnati.

 

“Kasafin kuɗin da ke gaban mu ba abin alfahari ba ne, idan an yi la’akari da abin da ake yi a wasu ƙasashe.

 

“Dole ne mu yi magana a matsayin ‘yan majalisa; dole ne mu ƙi amincewa da kasafin kuɗin ta hanyar kiran a ƙara yawan kasafin da aka ware wa ma’aikatar.

 

“Muna so Ministan Kasafi da Tsare-tsare na Ƙasa ya bayyana a gaban mu don sake duba kasafin kuɗin.”

 

A baya, ministan ya ƙiyasta cewa mafi ƙarancin adadin da ake buƙata don gudanar da ayyukan ma’aikatar yadda ya kamata ya kai naira biliyan 50.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
Labarai

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

October 31, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

October 31, 2025
Next Post
Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

October 31, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

October 31, 2025
Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa

October 31, 2025
Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa

October 31, 2025

Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda

October 31, 2025
Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi

Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi

October 31, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai

October 31, 2025
Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.