• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwangilar Tashar Wutar Mambila: Obasanjo Zai Bayar Da Shaida A Kotun Paris Yau

by Sadiq
5 months ago
in Manyan Labarai
0
Hujjojin Obasanjo Na Cewa “Dimokuradiyyar Turawan Yamma Ba Ta Karbi Afirka Ba”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo zai bayar da shaida a yau a gaban Kotun Kasuwanci ta Duniya (ICC) da ke birnin Paris kan shari’ar dala biliyan $2.3 da kamfanin Sunrise Power ya shigar da Nijeriya ƙara. 

Kamfanin ya zargi gwamnatin da karya yarjejeniyar da aka ƙulla a 2003 don gina babbar tashar wutar lantarki ta Mambilla mai darajar dala biliyan shida a Jihar Taraba.

  • Gwamnati Tarayya Ta Musanta Zargin Bai Wa Kamfanin Bogi Kwangilar Aikin Hanyar Abuja-Kano
  • Gobara Ta Hallaka Mutum 66 A Otal Mai Hawa 12 A Turkiyya

Taƙaddamar ta fara ne bayan da kamfanin Sunrise Power ya ce gwamnatin ta saɓa yarjejeniyar da suka ƙulla.

Obasanjo ya musanta cewa ya amince da yarjejeniyar a lokacin mulkinsa, yana mai cewa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Olu Agunloye, ya yi aiki ba tare da izininsa ba.

A 2017, Sunrise Power ya shigar da ƙarar, inda ya nemi a biya shi diyya.

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Duk da yarjejeniyar biyan dala miliyan 200 a wajen kotu da aka cimma a 2020, Sunrise daga baya ya nemi ƙarin diyyar dala miliyan 400, inda ya zargi gwamnati ta kasa cika alƙawari.

Lamarin shari’ar ya shafi wasu manyan mutane kamar tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari da Shugaban Sunrise Power, Leno Adesanya, wanda ya riga ya bayar da shaida a wannan mako.

Sakamakon shari’ar na iya yin tasiri sosai kan harkar wutar lantarki da kuma adadin diyyar da Nijeriya za ta biya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KamfaniKotuMambilaObasanjoParisShaida
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Musanta Zargin Bai Wa Kamfanin Bogi Kwangilar Aikin Hanyar Abuja-Kano

Next Post

An Sallami Saif Ali Khan Daga Asibiti Bayan Harin Da Aka Kai Masa

Related

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

33 minutes ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

2 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

2 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

7 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

18 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

20 hours ago
Next Post
An Sallami Saif Ali Khan Daga Asibiti Bayan Harin Da Aka Kai Masa

An Sallami Saif Ali Khan Daga Asibiti Bayan Harin Da Aka Kai Masa

LABARAI MASU NASABA

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.