• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Samar Da Rumbun Adana Bayanai Don Tallafa Wa Manoma

by Abubakar Abba
6 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, ta rattaba hannun yarjejeniya da Hukumar Bayar da Katin Shedar Dan Kasa (NIMC), domin kirkiro da rumbun adana bayanai, don bai wa manoma tallafin aikin noma.

Manufar shirin shi ne, kara habaka fannin aikin noma tare da samar da wadataccen abinci a Nijeriya, hakan kuwa; ya kasance cikin kudurori takwas na Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

  • Nazarin CGTN: Tsauraran Manufofin Amurka Na Shan Suka
  • Asibitin Aminu Kano Ya Musanta Cire Mahaifar Mara Lafiya Ba Tare Da Izini Ba

Rumbun, wanda za a yi masa lakabi da yi wa manoma rijista, za a bukaci amfani da daukar bayanan manoman, domin gano sahihan manoman da za su amfana da tallafin tare kuma da tabbatar da ganin sun mallaki gonaki.

A kashin farko na shirin, ana sa ran yi wa manoma miliyan biyu rijista cikin wata uku, inda kuma za a yi wa kashi na biyu su kimanin miliyan shida rijistar.

A cikin wata uku, Hukumar ta NIMC, za ta iya samun bayanan manoman tare da hada rukuni don cimma burin gudanar da shirin.

Labarai Masu Nasaba

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Har ila yau, don hukumar ta samu damar isa ga manoman wajen gudanar da shirin, za ta yi hadaka da kamfanoni masu zaman kansu tare kuma yin aiki da sauran ofisoshiinta da ke daukacin kanannan hukumomin wannan kasa.

Shirin ya kuma kunshi amfani da bayar da katin da za a yi amfani da shi, domin cire kudin tallafin noma ga manoman.

Babban Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Abubakar Kyari, ya bayyan haka ne a jawabinsa wajen taron rattaba hannun wannan yarjejeniyar da aka gudanar a shalkwatar ma’aiktar, ranar Laraba a babban birnin tarayya Abuja.

“Abin da muka rattaba hannun a halin yanzu da hukumar kasa da kasa shi ne, bunkasa yi wa manoma rijista”, in ji Kyari.

Kazalika, ya kara da cewa; za mu yi amfani da manhajar rumbun adana bayanai na Hukumar NIMC, domin samar da katin shedar dan kasa (NIN), tare kuma da sama wa manoman katin da zai dauki bayanansu.

“Da farko dai, za mu gano gonakin da manoman suka mallaka tare da yin nomansu, wanda hakan zai ba mu damar sanin gonakin da suke nomawa, domin yi su rijistar”, a cewar Kyari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: gwamnatiNomaRumbu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nazarin CGTN: Amurka Na Dora Laifin Gazawar Shugabancinta Kan Bakin Haure

Next Post

An Gudanar Da Shirye-Shiryen Musammam Na CMG A Spaniya Da Brazil Gabanin Bikin Bazara

Related

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

1 day ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

1 day ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

1 week ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

1 week ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Next Post
An Gudanar Da Shirye-Shiryen Musammam Na CMG A Spaniya Da Brazil Gabanin Bikin Bazara

An Gudanar Da Shirye-Shiryen Musammam Na CMG A Spaniya Da Brazil Gabanin Bikin Bazara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.