• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaftace Soshiyyal Midiya: Kawu Ya Shirya Taron Kawo Gyara A Kano

by Sadiq
8 months ago
in Siyasa
0
Tsaftace Soshiyyal Midiya: Kawu Ya Shirya Taron Kawo Gyara A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙoƙarinsa na kawo gyara ga yadda ake amfani da soshiyal midiya, musamman a tsakanin ‘yan siyasa da magoya bayansu, tsohon ɗan Majalisar Wakilai daga Ƙaramar Hukumar Tarauni a Jihar Kano, Alhaji Hafizu Kawu, ya shirya wata bita ta musamman. 

Taron, wanda aka shirya ƙarƙashin ‘Hafizu Kawu Media Team’ tare da haɗin gwiwar Majalisar Malamai ta Kano, ya mayar da hankali kan buƙatar tsaftace mu’amalar jama’a a kafafen sada zumunta.

  • ‘Yan Nijeriya Za Su Maka Gwamnati A Kotu Kan Karin Kudin Kiran Waya
  • Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

A cewar Hafizu Kawu, “Mun lura cewa yadda ake amfani da soshiyal midiya yanzu ya wuce inda ya kamata, musamman a siyasa.

“Wannan ya sa muka ga dacewar gayyatar malamai, waɗanda za su taimaka wajen wayar da kai game da muhimmancin zumunci da mutuntawa. Siyasa bai kamata ta zama hanyar raba kan al’umma ba.”

Dalilin Shirya Bitar

Da yake ƙarin bayani kan dalilin shirya bitar, Hafizu Kawu ya ce, “Bature ya ƙirƙiro soshiyal midiya ne domin sada zumunta da isar da saƙo cikin sauƙi.

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

“Amma mun ga yadda ake amfani da ita wajen yaɗa fitina da cin zarafi, wanda hakan ba daidai ba ne a addininmu.

“Wannan shi ya sa muka yi wannan taro domin ilmantarwa, domin magoya bayan jam’iyyu daban-daban su fahimci muhimmancin adawa mai tsafta da mutuntawa.”

Ya ƙara da cewa, “Mun gayyaci malamai kamar Sheikh Ibrahim Khalil, Dokta Aminu Daurawa, da Farfesa Abdallah Uba Adamu saboda su taimaka wajen faɗakarwa da ilmantar da jama’a.

“Malamai ne ke da tasiri wajen wayar da kan jama’a, kuma mun gode da irin gudunmawar da suke bayarwa.”

Ra’ayoyin Jama’a Kan Bitar

Game da martanin jama’a kan bitar, Hafizu Kawu ya bayyana cewa taron ya samu karɓuwa sosai.

Ya ce, “Mutane sun yaba da taron. Wasu ma sun ce da sun sani sun halarta, saboda ba a taɓa samun irin wannan ba a Kano.

“Mun samu damar haɗuwa da ‘yan siyasa daga ɓangarorin daban-daban tare da malamai domin tsaftace harkar soshiyal midiya.”

Kawu ya kuma bayyana cewa akwai buƙatar faɗaɗa irin wannan bita nan gaba ta hanyar gayyatar jami’an tsaro da shugabanni da masu ruwa da tsaki.

Amfanin Taron Ga Jama’a

A cewar Hafizu Kawu, babban amfanin wannan taro shi ne ƙara fahimtar juna da kuma rage rigingimu a tsakanin ‘yan siyasa da magoya bayansu.

Ya ce, “Adawa halal ce, amma ta zama wajibi a yi ta cikin mutuntawa da gyara. Wannan zai taimaka wajen magance rigingimu, cin zarafi, da haddasa husuma.

“Kuma zai sa ‘yan siyasa su fahimci yadda za su yi amfani da soshiyal midiya don tallata manufofinsu ba tare da raba kan jama’a ba.”

Makomar Soshiyal Midiya a Siyasar Nijeriya

Hafizu Kawu ya ja hankalin shugabanni kan buƙatar wayar da kan matasa game da amfani da soshiyal midiya.

“Yanzu haka soshiyal midiya ita ce abin da ke karaɗe duniya. Dole ne mu ƙara dagewa wajen ilmantarwa da faɗakarwa domin kada mu tsinci kanmu a cikin wani hali da ba ma so.”

Ya kammala da cewa, “Dole ne gwamnatoci su bayar da goyon baya ga irin wannan hoɓɓasa, domin kare al’umma daga illolin amfani da soshiyal midiya ba tare da tsafta ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BitaHafizu KawuSiyasaSoshiyyal MidiyaTaroTsohon Ɗan Majalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Sana’ar POS Za Su Kara Kudin Caji, Sakamakon Karin Kudin Kira Da Na Data

Next Post

Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

16 hours ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

1 day ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

2 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

3 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

5 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

7 days ago
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.