ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaftace Soshiyyal Midiya: Kawu Ya Shirya Taron Kawo Gyara A Kano

by Sadiq
1 year ago
Soshiyyal Midiya

A ƙoƙarinsa na kawo gyara ga yadda ake amfani da soshiyal midiya, musamman a tsakanin ‘yan siyasa da magoya bayansu, tsohon ɗan Majalisar Wakilai daga Ƙaramar Hukumar Tarauni a Jihar Kano, Alhaji Hafizu Kawu, ya shirya wata bita ta musamman. 

Taron, wanda aka shirya ƙarƙashin ‘Hafizu Kawu Media Team’ tare da haɗin gwiwar Majalisar Malamai ta Kano, ya mayar da hankali kan buƙatar tsaftace mu’amalar jama’a a kafafen sada zumunta.

  • ‘Yan Nijeriya Za Su Maka Gwamnati A Kotu Kan Karin Kudin Kiran Waya
  • Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

A cewar Hafizu Kawu, “Mun lura cewa yadda ake amfani da soshiyal midiya yanzu ya wuce inda ya kamata, musamman a siyasa.

ADVERTISEMENT

“Wannan ya sa muka ga dacewar gayyatar malamai, waɗanda za su taimaka wajen wayar da kai game da muhimmancin zumunci da mutuntawa. Siyasa bai kamata ta zama hanyar raba kan al’umma ba.”

Dalilin Shirya Bitar

Da yake ƙarin bayani kan dalilin shirya bitar, Hafizu Kawu ya ce, “Bature ya ƙirƙiro soshiyal midiya ne domin sada zumunta da isar da saƙo cikin sauƙi.

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

“Amma mun ga yadda ake amfani da ita wajen yaɗa fitina da cin zarafi, wanda hakan ba daidai ba ne a addininmu.

“Wannan shi ya sa muka yi wannan taro domin ilmantarwa, domin magoya bayan jam’iyyu daban-daban su fahimci muhimmancin adawa mai tsafta da mutuntawa.”

Ya ƙara da cewa, “Mun gayyaci malamai kamar Sheikh Ibrahim Khalil, Dokta Aminu Daurawa, da Farfesa Abdallah Uba Adamu saboda su taimaka wajen faɗakarwa da ilmantar da jama’a.

“Malamai ne ke da tasiri wajen wayar da kan jama’a, kuma mun gode da irin gudunmawar da suke bayarwa.”

Ra’ayoyin Jama’a Kan Bitar

Game da martanin jama’a kan bitar, Hafizu Kawu ya bayyana cewa taron ya samu karɓuwa sosai.

Ya ce, “Mutane sun yaba da taron. Wasu ma sun ce da sun sani sun halarta, saboda ba a taɓa samun irin wannan ba a Kano.

“Mun samu damar haɗuwa da ‘yan siyasa daga ɓangarorin daban-daban tare da malamai domin tsaftace harkar soshiyal midiya.”

Kawu ya kuma bayyana cewa akwai buƙatar faɗaɗa irin wannan bita nan gaba ta hanyar gayyatar jami’an tsaro da shugabanni da masu ruwa da tsaki.

Amfanin Taron Ga Jama’a

A cewar Hafizu Kawu, babban amfanin wannan taro shi ne ƙara fahimtar juna da kuma rage rigingimu a tsakanin ‘yan siyasa da magoya bayansu.

Ya ce, “Adawa halal ce, amma ta zama wajibi a yi ta cikin mutuntawa da gyara. Wannan zai taimaka wajen magance rigingimu, cin zarafi, da haddasa husuma.

“Kuma zai sa ‘yan siyasa su fahimci yadda za su yi amfani da soshiyal midiya don tallata manufofinsu ba tare da raba kan jama’a ba.”

Makomar Soshiyal Midiya a Siyasar Nijeriya

Hafizu Kawu ya ja hankalin shugabanni kan buƙatar wayar da kan matasa game da amfani da soshiyal midiya.

“Yanzu haka soshiyal midiya ita ce abin da ke karaɗe duniya. Dole ne mu ƙara dagewa wajen ilmantarwa da faɗakarwa domin kada mu tsinci kanmu a cikin wani hali da ba ma so.”

Ya kammala da cewa, “Dole ne gwamnatoci su bayar da goyon baya ga irin wannan hoɓɓasa, domin kare al’umma daga illolin amfani da soshiyal midiya ba tare da tsafta ba.”

MASU ALAKA

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
Siyasa

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano
Siyasa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

LABARAI MASU NASABA

Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.