ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaftace Soshiyyal Midiya: Kawu Ya Shirya Taron Kawo Gyara A Kano

by Sadiq
1 year ago
Soshiyyal Midiya

A ƙoƙarinsa na kawo gyara ga yadda ake amfani da soshiyal midiya, musamman a tsakanin ‘yan siyasa da magoya bayansu, tsohon ɗan Majalisar Wakilai daga Ƙaramar Hukumar Tarauni a Jihar Kano, Alhaji Hafizu Kawu, ya shirya wata bita ta musamman. 

Taron, wanda aka shirya ƙarƙashin ‘Hafizu Kawu Media Team’ tare da haɗin gwiwar Majalisar Malamai ta Kano, ya mayar da hankali kan buƙatar tsaftace mu’amalar jama’a a kafafen sada zumunta.

  • ‘Yan Nijeriya Za Su Maka Gwamnati A Kotu Kan Karin Kudin Kiran Waya
  • Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

A cewar Hafizu Kawu, “Mun lura cewa yadda ake amfani da soshiyal midiya yanzu ya wuce inda ya kamata, musamman a siyasa.

ADVERTISEMENT

“Wannan ya sa muka ga dacewar gayyatar malamai, waɗanda za su taimaka wajen wayar da kai game da muhimmancin zumunci da mutuntawa. Siyasa bai kamata ta zama hanyar raba kan al’umma ba.”

Dalilin Shirya Bitar

Da yake ƙarin bayani kan dalilin shirya bitar, Hafizu Kawu ya ce, “Bature ya ƙirƙiro soshiyal midiya ne domin sada zumunta da isar da saƙo cikin sauƙi.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

“Amma mun ga yadda ake amfani da ita wajen yaɗa fitina da cin zarafi, wanda hakan ba daidai ba ne a addininmu.

“Wannan shi ya sa muka yi wannan taro domin ilmantarwa, domin magoya bayan jam’iyyu daban-daban su fahimci muhimmancin adawa mai tsafta da mutuntawa.”

Ya ƙara da cewa, “Mun gayyaci malamai kamar Sheikh Ibrahim Khalil, Dokta Aminu Daurawa, da Farfesa Abdallah Uba Adamu saboda su taimaka wajen faɗakarwa da ilmantar da jama’a.

“Malamai ne ke da tasiri wajen wayar da kan jama’a, kuma mun gode da irin gudunmawar da suke bayarwa.”

Ra’ayoyin Jama’a Kan Bitar

Game da martanin jama’a kan bitar, Hafizu Kawu ya bayyana cewa taron ya samu karɓuwa sosai.

Ya ce, “Mutane sun yaba da taron. Wasu ma sun ce da sun sani sun halarta, saboda ba a taɓa samun irin wannan ba a Kano.

“Mun samu damar haɗuwa da ‘yan siyasa daga ɓangarorin daban-daban tare da malamai domin tsaftace harkar soshiyal midiya.”

Kawu ya kuma bayyana cewa akwai buƙatar faɗaɗa irin wannan bita nan gaba ta hanyar gayyatar jami’an tsaro da shugabanni da masu ruwa da tsaki.

Amfanin Taron Ga Jama’a

A cewar Hafizu Kawu, babban amfanin wannan taro shi ne ƙara fahimtar juna da kuma rage rigingimu a tsakanin ‘yan siyasa da magoya bayansu.

Ya ce, “Adawa halal ce, amma ta zama wajibi a yi ta cikin mutuntawa da gyara. Wannan zai taimaka wajen magance rigingimu, cin zarafi, da haddasa husuma.

“Kuma zai sa ‘yan siyasa su fahimci yadda za su yi amfani da soshiyal midiya don tallata manufofinsu ba tare da raba kan jama’a ba.”

Makomar Soshiyal Midiya a Siyasar Nijeriya

Hafizu Kawu ya ja hankalin shugabanni kan buƙatar wayar da kan matasa game da amfani da soshiyal midiya.

“Yanzu haka soshiyal midiya ita ce abin da ke karaɗe duniya. Dole ne mu ƙara dagewa wajen ilmantarwa da faɗakarwa domin kada mu tsinci kanmu a cikin wani hali da ba ma so.”

Ya kammala da cewa, “Dole ne gwamnatoci su bayar da goyon baya ga irin wannan hoɓɓasa, domin kare al’umma daga illolin amfani da soshiyal midiya ba tare da tsafta ba.”

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.