ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaftace Soshiyyal Midiya: Kawu Ya Shirya Taron Kawo Gyara A Kano

by Sadiq
1 year ago
Soshiyyal Midiya

A ƙoƙarinsa na kawo gyara ga yadda ake amfani da soshiyal midiya, musamman a tsakanin ‘yan siyasa da magoya bayansu, tsohon ɗan Majalisar Wakilai daga Ƙaramar Hukumar Tarauni a Jihar Kano, Alhaji Hafizu Kawu, ya shirya wata bita ta musamman. 

Taron, wanda aka shirya ƙarƙashin ‘Hafizu Kawu Media Team’ tare da haɗin gwiwar Majalisar Malamai ta Kano, ya mayar da hankali kan buƙatar tsaftace mu’amalar jama’a a kafafen sada zumunta.

  • ‘Yan Nijeriya Za Su Maka Gwamnati A Kotu Kan Karin Kudin Kiran Waya
  • Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

A cewar Hafizu Kawu, “Mun lura cewa yadda ake amfani da soshiyal midiya yanzu ya wuce inda ya kamata, musamman a siyasa.

ADVERTISEMENT

“Wannan ya sa muka ga dacewar gayyatar malamai, waɗanda za su taimaka wajen wayar da kai game da muhimmancin zumunci da mutuntawa. Siyasa bai kamata ta zama hanyar raba kan al’umma ba.”

Dalilin Shirya Bitar

Da yake ƙarin bayani kan dalilin shirya bitar, Hafizu Kawu ya ce, “Bature ya ƙirƙiro soshiyal midiya ne domin sada zumunta da isar da saƙo cikin sauƙi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

“Amma mun ga yadda ake amfani da ita wajen yaɗa fitina da cin zarafi, wanda hakan ba daidai ba ne a addininmu.

“Wannan shi ya sa muka yi wannan taro domin ilmantarwa, domin magoya bayan jam’iyyu daban-daban su fahimci muhimmancin adawa mai tsafta da mutuntawa.”

Ya ƙara da cewa, “Mun gayyaci malamai kamar Sheikh Ibrahim Khalil, Dokta Aminu Daurawa, da Farfesa Abdallah Uba Adamu saboda su taimaka wajen faɗakarwa da ilmantar da jama’a.

“Malamai ne ke da tasiri wajen wayar da kan jama’a, kuma mun gode da irin gudunmawar da suke bayarwa.”

Ra’ayoyin Jama’a Kan Bitar

Game da martanin jama’a kan bitar, Hafizu Kawu ya bayyana cewa taron ya samu karɓuwa sosai.

Ya ce, “Mutane sun yaba da taron. Wasu ma sun ce da sun sani sun halarta, saboda ba a taɓa samun irin wannan ba a Kano.

“Mun samu damar haɗuwa da ‘yan siyasa daga ɓangarorin daban-daban tare da malamai domin tsaftace harkar soshiyal midiya.”

Kawu ya kuma bayyana cewa akwai buƙatar faɗaɗa irin wannan bita nan gaba ta hanyar gayyatar jami’an tsaro da shugabanni da masu ruwa da tsaki.

Amfanin Taron Ga Jama’a

A cewar Hafizu Kawu, babban amfanin wannan taro shi ne ƙara fahimtar juna da kuma rage rigingimu a tsakanin ‘yan siyasa da magoya bayansu.

Ya ce, “Adawa halal ce, amma ta zama wajibi a yi ta cikin mutuntawa da gyara. Wannan zai taimaka wajen magance rigingimu, cin zarafi, da haddasa husuma.

“Kuma zai sa ‘yan siyasa su fahimci yadda za su yi amfani da soshiyal midiya don tallata manufofinsu ba tare da raba kan jama’a ba.”

Makomar Soshiyal Midiya a Siyasar Nijeriya

Hafizu Kawu ya ja hankalin shugabanni kan buƙatar wayar da kan matasa game da amfani da soshiyal midiya.

“Yanzu haka soshiyal midiya ita ce abin da ke karaɗe duniya. Dole ne mu ƙara dagewa wajen ilmantarwa da faɗakarwa domin kada mu tsinci kanmu a cikin wani hali da ba ma so.”

Ya kammala da cewa, “Dole ne gwamnatoci su bayar da goyon baya ga irin wannan hoɓɓasa, domin kare al’umma daga illolin amfani da soshiyal midiya ba tare da tsafta ba.”

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

Majalisar Wakilai Ta Gabatar Da Ƙudirori 15 Don Magance Yunwa

LABARAI MASU NASABA

Hisbah

Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah

July 22, 2026
An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

An Karyata Maganar Wai Akwai “Matsin Kasar Sin”

July 22, 2026
Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

Sojoji Sun Daƙile ‘Yan Ta’adda Daga Karɓar Haraji A Yobe

July 22, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wasu Da Aka Sace A Zamfara, Katsina Da Kebbi

July 22, 2026
NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

NNPP Ta Yi Barazanar Maka INEC A Kotu Kan Ƙin Bin Umarnin Dawo Da Tambarinta A Kan Lokaci

July 22, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

Shugaban Laliga Ya Buƙaci Infantino Ya Sauka Daga Shugabancin FIFA

July 22, 2026
Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

Kasar Sin: Yunkurin Japan Na Kalubalantar Odar Kasa Da Kasa Bayan Yakin Duniya Na Biyu A Bayyana Yake Kasa

July 21, 2026
Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

Babban Jami’in Diflomasiyyar Sin Ya Jaddada Matsayar Dangantakar Kasar Da Turai Ta Hadin Gwiwa

July 21, 2026
Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

Yayin Da Na’ura Ta Fara Tunani: Bil’adama Ne Kadai Zai Iya Tunkarar Lamarinta

July 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.