• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Harkokin Tsaro Sun Soki Shirin Dawo Da Tubabbun ‘Yan Ta’adda Cikin Al’umma

by Sani Anwar
7 months ago
in Tsaro
0
Masana Harkokin Tsaro Sun Soki Shirin Dawo Da Tubabbun ‘Yan Ta’adda Cikin Al’umma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masana harkokin tsaro da kungiyoyi masu zaman kansu da kuma wadanda ta’addancin ya shafa, sun bayyana rashin jin dadinsu na yadda ‘yan ta’addan Boko Haram suka koma cikin al’umma, don ci gaba da gudanar da rayuwarsu; ba tare da la’akari da wadanda suka sanya cikin halin ha’ula’i ba.

An zargi gwamnatin kasar da yi wa tubabbun ’yan kungiyar goma ta arziki, yayin da kuma wadanda zalincin nasu ya shafa ke cikin kunci a sansanoninsu na ‘yan gudun hijira da ke fadin wannan kasa.

Wani mai ba da shawara a kan harkokin tsaro, Abdullahi Mohammed Jabi, ya caccaki yadda aka dawo da tubabbun ‘yan ta’addan su kimanin 5000, cikin al’ummar da suka tava kai wa hare-haren ta’addanci.

  • Babu Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Tsarinmu – Gwamnan Zamfara
  • Dogaro Da Kasashen Yamma Ba Zai Tabbatar Da Tsaro A Philippines Ba

Ya ce, wannan matakin da aka dauka ya kawo cikas ga sadaukarwar da ‘yan Nijeriya masu kishin kasa suka yi, wadanda suka bayar da gagarumar gudunmawa wajen kare kasar.

A baya-bayan nan dai, an kashe sojojin kasar kimanin 22; ciki har da kwamanda a Borno, a ranar 25 ga watan Janairun 2025, a wani farmaki da suka kai wa ‘yan ta’addan a wani waje da ake kira ‘Timbuktu Triangle’, bayan ‘yan ta’addan sun baza ‘yan kunar-bakin-wake a cikin motoci dauke da bamabamai, don kakkave sojojin.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Sai dai kuma, bayan bayyana a taron da gwamnonin tafkin Chadi suka yi a Borno na cewa, tubabbun ‘yan ta’adda sama 5000 ne suka sake haduwa da iyalansu, Jabi ya ce; babu shakka wannan wani cin fuska ne ga fuskokin wadanda aka kashe da kuma jaruman sojojin da suka mutu.

tsaro

Haka nan, ya kuma sake bayyana hadewar komawar tasu cikin al’umma a matsayin wani babban kuskure wajen aiwatar da manufofin da suka dace.

Ya kara da cewa, “Abin da ya kamata mu yi wa ‘yan ta’adda shi ne, mu tabbata sun girbi abin da suka shuka. Saboda haka, idan har da gaske muke wajen kawar da ta’addanci a fadin wannan kasa, ya kamata mu sanya ido yadda ya kamata. Bana goyon bayan wannan abu da ake kira; sake shigar da ‘yan ta’adda cikin al’umma da siyasa.

“Wannan ba daidai ba ne, kuskure ne. Wadannan mutane, babu wani ci gaba da za su kawo wa kasa ko al’ummar da ke cikinta, in ban da kara dagula al’amura da za su yi”, a cewarsa.

Jabi ya ci gaba da cewa, sakamakon ayyukan ‘yan ta’adda, manoman da ya kamata a ce suna samar wa al’umma abinci; suna can sansanonin ‘yan gudun hijira suna rayuwa cikin mawuyacin hali.

Wani dan asalin Jihar Yobe, wanda ba ya so a bayyana sunansa, saboda fargabar ramuwar gayya; ya nuna rashin jin dadinsa ga gwamnatin tarayya da na jihohi, dangane da shirin sake dawo da wadannan ‘yan ta’adda cikin al’umma.

Ya ce, kyautuwa ya yi gwamnatin tarayya a ce tuni ta kammala fatattakar wadannan ‘yan ta’adda, kafin ta kai ga fara aiwatar da wannan shi.

Shi ma a nasa vangaren, babban daraktan cibiyar kare hakkin al’umma (CISLAC), Auwal Musa Rafsanjani ya ce, mayar da ‘yan ta’addan da suka tuba, ba tare da sake tsugunar da wadanda ta’addacin ya shafa ba, abu ne da zai tava samun karvuwa ba.

Don haka, ya yi kira ga gwamnati da ta gurfanar da duk wadanda suka taka rawa wajen cin zarafin al’umma tare da tabbatar da adalci.

Sanusi Isa, daraktan kungiyar ‘Amnesty International’ ta kasa, shi ma ya yi magana makwatankwaciyar wannan, inda ya yi nuni da cewa, duk wadanda suka aikata laifuka; su fuskanci hukunci na gaskiya.

Sannan ya kara da cewa, dukkanin wadanda abin ya shafa da wadanda suka tsira da iyalansu, sun cancanci a yi musu adalci.

daya daga cikin Shugabannin al’ummar Chibok, Mutah Nkeki, ya bayyana ra’ayinsa a matsayin rashin adalci da gwamnati ta shirya a kan ‘yan asalin Chibok da sauran daukacin wadanda ta’addancin ya shafa.

Ya yi zargin cewa, ‘yan matan makarantar Chibok da Boko Haram suka sace a shekarar 2014, an hana su ganawa da shugabanni da kuma iyayensu, tun bayan da suka tsere daga hannunsu.

Har ila yau, ya kara da cewa, babban abin takaicin shi ne, faruwar lamarin ya jawo mutuwar iyaye dama, inda y ace wadanda ke raye; ba a bas u damar ganin ‘ya’yansu mata da suka kuvuta ko aka kuvutar da su ba.  

Da aka tuntuvi kwamishinan yada labarai da tsaron cikin gida na Jihar Borno, Farfesa Usman Tar; ya musanta dukkanin zarge-zargen.

Ya ce, savanin zargin da ake yi; gwamnati jihar ta bayar da makudan kudade, domin sake tsugunar da al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihohi 29 Sun Yi Watsi Da Ayyuka 270 Na Biliyoyin Naira

Next Post

Hakuri Da Baiwa (Kyautar) Manzon Allah (SAW)

Related

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

3 days ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

3 days ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

1 week ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

1 week ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

1 week ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

2 weeks ago
Next Post
Hakuri Da Baiwa (Kyautar) Manzon Allah (SAW)

Hakuri Da Baiwa (Kyautar) Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.