• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gudanar Da Zauren Tattaunawa Na Ministoci Karo Na Biyu

by Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gudanar Da Zauren Tattaunawa Na Ministoci Karo Na Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ta fara zagaye na biyu na Zauren Tattaunawa na Ministoci, inda Ministan Raya Kiwon Dabbobi, Alhaji Idi Mukhtar; da Ministan Cigaban Yankuna, Injiniya Abubakar Eshiokpekha Momoh, da Ƙaramin Ministan sa, Alhaji Uba Maigari Ahmadu, suka gabatar da jawabai kan ayyukan ma’aikatun su.  

 

Da yake gabatar da jawabin maraba, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana wannan zama da aka yi ranar Juma’a a matsayin dandalin da ke bajekolin nasarorin da Gwamnatin Tinubu ta cimma a fannoni daban-daban.

  • KACCIMA Za Ta Baje Kolin Kayan Abincin Azumi Don Saukaka Wa Al’umma – Sidiya Gambo
  • Saudiyya Za Ta Haramta Shan Giya Lokacin Gasar Kofin Duniya

Ya ce: “Ina maku maraba da zuwa zagaye na biyu na Zauren Tattaunawa na Ministoci na shekarar 2025. Kamar yadda kuka sani, a ranar Talata, 11 ga Fabrairu, 2025, na ƙaddamar da wannan jerin tarurruka na bana, inda na jaddada manyan nasarorin da aka cimma a ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.”

 

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

Ya ce Ma’aikatar Raya Kiwon Dabbobi da ta Cigaban Yankuna suna daga cikin sababbin ma’aikatun da Shugaban Ƙasa Tinubu ya ƙirƙira domin bunƙasa fannin kiwo da haɓaka cigaban yankuna a Nijeriya.

 

Ya ce: “Waɗannan ma’aikatun guda biyu su ne sababbi a ƙasar. An kafa Ma’aikatar Raya Kiwon Dabbobi a watan Yulin 2024 domin sauya damar kiwon dabbobi mai darajar biliyoyin daloli zuwa ingantaccen cigaban tattalin arziki ga ‘yan Nijeriya.

 

“Haka nan, an kafa Ma’aikatar Raya Yankuna a watan Oktoban 2024 domin kula da ayyukan hukumomin raya yankuna a faɗin ƙasar nan.

Tarayya

“Tun bayan kafuwar waɗannan ma’aikatun, ministocin sun fara aiki da himma, kuma sun zo a yau domin ƙarin bayani kan abin da suka aiwatar tun daga lokacin da aka ƙirƙiri ma’aikatun nasu.”

 

Ministan ya yaba da rawar da ‘yan jarida ke takawa wajen yaɗa labaran zaman tattaunawar ministocin, yana mai cewa su ne ginshiƙin isar da sahihan bayanai ga ‘yan Nijeriya.

 

Ya kuma buƙaci ‘yan jarida da su guji yaɗa rahotannin da ke da ruɗani ko kwaskwarima.

 

Ya ce: “Kafofin watsa labarai sun kasance abokan hulɗar da ba za a iya musantawa ba a ƙoƙarin mu na ci gaba da sanar da ‘yan Nijeriya kan manyan nasarorin da Gwamnatin Tinubu ta cimma.

 

“Ina kira ga ‘yan jarida da su tabbatar da cewa rahotannin da suka shafi waɗannan tarurruka na bayar da bayanai ana gabatar da su da cikakken adalci da inganci.

 

“Bai kamata a riƙa cusa son rai ko ɓata gaskiya wajen rahoto kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati ba.

 

“Yana da kyau a samu sukar ra’ayi da bambancin fahimta domin dimokiraɗiyya, amma kada a bari ji-ta-ji-ta da karkatar da gaskiya su samu gurbi a muhawarar jama’a.”

 

Ya tabbatar da cewa gwamnati za ta yaɗa bayanan wannan zaman tattaunawar ta kafafen yaɗa labarai daban-daban domin tabbatar da gaskiya da karɓar ra’ayoyin jama’a.

 

Za a ci gaba da shirye-shiryen Zauren Tattaunawa na Ministocin, inda manyan jami’an gwamnati za su riƙa gabatar da bayanai kan cigaban da ake samu a fannoni daban-daban.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ake Haɗa Kayan Ƙamshi Na Miya (Spices)

Next Post

David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa – Amorim

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

2 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

5 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

7 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

8 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

10 hours ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

11 hours ago
Next Post
David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa – Amorim

David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa - Amorim

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Tarayya

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.