ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
11 months ago
Sailuba

Shafin Rumbun Nishadi, yau kuma yana tafe ne da daya daga cikin jarumai masu tasowa a halin yanzu, wato Nusaiba Muhammad Ibrahim, wacce aka fi sani da Sailuba a cikin shirin Dadin Kowa, inda ta bayyana wa masu karatu irin nasarorin da ta samu game da harkar fim, har ma da wasu batutuwan da suka shafi sana’ar tata ta fim.

Ga dai tattaunawar tare da wakiliyarmu, Rabi’at Sidi Bala, kamar haka:

Ko za ki fada wa masu karatu cikakkenan sunanki da kuma sunan da aka fi sanin ki da shi?

ADVERTISEMENT

Sunana Nusaiba Muhammad Ibrahim, amma an fi sanina da Sailuba Dadin Kowa.

 

LABARAI MASU NASABA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Masu karatu za su so jin dan takaitaccen tarihinki?

An haife ni a garin Gombe, amma sai daga bisani na bar garin Gomben da zama na dawo Kano, tun ina ‘yar shekara biyar da haihuwa, sakamakon mahaifina yana aiki a Kanon. Kazalika, na girma a gaban iyayena, na yi firamare da sakandare duk a garin Kano, sannan kuma ban taba yin aure ba; budurwa ce ni.

 

Wace irin rawa kike takawa a cikin masana’antar shirya finafinai ta Kannywood?

Ina fitowa ne a matsayin Jaruma kawai, amma kuma ina da niyyar zama mai bayar da umarni a nan gaba kadan insha Allah.

 

Me ya ja hankalinki, har kika tsunduma harkar fim?

Wato batu na gaskiya, fim yana burge ni kwarai da gaske, amma dalilin shigata sana’ar ita ce; wani fim aka yi sai wata arniyya ta musulunta, daga nan ne na ce; in dai har fim yana isar da sako, har ya zama silar gyaruwar al’umma, gaskiya zan zama daya daga cikin wadanda za su isar da wannan sako, tunda da ma raina yana so matuka gaya.

 

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance?

Gaskiya ni ban sha wahala ba, dalili kuwa shi ne; dan fim ne ya sa ni a harkar ta fim, sannan kuma kamar yaya yake a wajena, dan Unguwarmu ne, iyayena da nasa sun zama kamar ‘yan’uwa.

 

Lokacin da kika fara sanar wa iyayenki cewa, kina son shiga harkar fim, wane kalubale da kika fuskanta daga wurinsu? 

Eh! Gaskiya na fuskanci kalubale, amma daga baya sun fahimce ni, sakamakon iyayen nawa masu fahimta ne.

 

Za ki yi kamar shekara nawa da fara fim?

Ina ga zan samu kamar shekara takwas da farawa.

 

Ya farkon fara dora miki Kyamara ya kasance?

Ban ji tsoron komai ba, kuma Alhamdulillahi na samu yabo sosai daga wajen masu bayar da umarni da sauran abokan aiki.

 

Wane fim kika fara yi a farkon zuwanki?

Na fara ne da fim din Dadin Kowa.

 

Wace rawa kika taka a cikin shirin na Dadin Kowa?

Na fito ne matsayin Sailuba, inda na taka rawa a matsayin matar aure. Surukata ce ta auro wa mijina ni a kauye, saboda ba ta son matar dan nata da aura, sakamakon cewa; Beyerabiya ce, wato maman Rasaki kenan, ni kuma a nan na yi ta tsula tsiyata.

 

Bayan da aka fara haska fuskarki cikin shirin Dadin Kowa, ya kika ji a lokacin, sannan kuma yaya kika kasance da mutanen Unguwarku da sauran ‘yan’uwa?

Alhamdulillah! Wadanda suka san ni a gaske, sun biyo ni har gida suna kallona kamar a da ba su san ni ba, wadanda kuma ba su san ni ba, idan muka hadu abin ba dama, ga tarin alhairai daga masoya daga gurare daban-daban.

 

Bayan shirin Dadin Kowa da kika fito a ciki, ko akwai wasu fina-finan da kika fito ciki?

Eh, na yi wasu fina-finan da dama.

 

Kamar wadanne kenan?

Kamar irin su: Ni da Mijin Yayata, Matar Waye, Zaman Tare, Matar Kaddara da dai sauransu, dukkanninsu masu masu dogon zango ne kuma ni ce jarumar ciki.

 

Cikin wadannan fina-finai da kika zayyano, wane fim ne ya fi burge ki, kuma me yasa, sannan wace rawa kika taka a cikin shirin?

Ni da mijin Yayata, na fito ne a matsayin budurwa wacce take matukar son mijin yayarta.

 

Ya kika ji a lokacin da za ki taka rawa a wannan shirin?

Na ji dadi sosai, saboda zan yi abin da nake so; sannan kuma an kara min kwarin gwiwa, har muka yi muka gama babu wata matsala.

 

Ya batun masu kallo bayan shirin ya fita, ko kin samu wani kalubale daga gare su?

A a, kawai dai idan aka gan ni a zahiri, a kan yi mamaki tare da bayyana cewa; na fi kyau a fili, wasu ma har su ce ba su yi zaton cewa; ‘yar birni ba ce ni, sun yi zaton yadda nake ‘yar kauye a Dadin Kowa, a gaske ma haka nake.

 

A fina-finan da kika yi, wane fim ne ya fi haska ki; har mutane suke iya gane ki?

Dadin Kowa, sai kuma wannan fim din na Matar Waye, shi ma ba abin da zan ce gaskiya.

 

Ko akwai wani kalubale da kika taba fuskanta, tun daga farkon zuwanki cikin masana’antar zuwa yanzu?

Gaskiya an samu, amma a da ne; yanzu cikin ikon Allah an samu daidaito.

 

Wadane irin nasarori kika samu game da fim?

Akwai nasarori da dama kamar ta fuskar samun kudi, mota, kayan sakawa, turaruka da sauran makamantansu.

 

Ko kina da ubangida a masana’antar Kannywood?

Kwarai da gaske ina da su, akwai Adam Musa Adam da kuma Usman Adam Hali Dubu.

 

Kafin ki fara fim, wadane jarumai ne suka fi burge ki har kike jin dama ki zama tamkar su?

Ina kowace jaruma, domin kuwa dukkaninsu suna burge ni.

 

Yaushe kike sa ran yin aure?

Duk lokacin da Allah ya kawo shi, a shirye nake.

 

Ko akwai wanda ya taba cewa yana son ki zai aure ki a masana’antar?

Kwarai da gaske, akwai.

 

Ko za mu iya jin sunansa?

A’a gaskiya.

 

Mene ne ra’ayinki game da auren dan fim?

Zan iya aurensa mana, ai babu wata matsala a ciki.

 

Wane irin namiji kike so ki aura?

Ya kasance Musulmi, mai ilimi, wanda kuma yake da cikakkiyar sana’a.

 

Wace shawara za ki bai wa abokan aikinki na masana’antar Kannywood?

Da farko dai, ya kamata mu hada kanmu, sannan mu kiyaye abin da zai bata sunan sana’ar tamu, mu kuma yi kokari wajen kare mutuncinmu, wannan shi ne a takaice.

 

Wacce shawara za ki bawa masu kokarin shigowa wannan masana’anta?

Su tabbata sun shigo da niyya mai kyau, sannan kuma su yarda cewa; sana’a suka zo yi, ba wani abu daban ba.

 

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

Ina fatan alhairi ga kowa da kowa, musamman masoyana.

Sailuba
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Lionel Messi: Mutum Ko Aljan
Sailuba
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kudin Shigar Gwamnatin Sin Ya Karu Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Zai Halarci Taron Dandalin Tattaunawar Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 17
  • Sulaiman
    Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

MASU ALAKA

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

LABARAI MASU NASABA

Kudin Shigar Gwamnatin Sin Ya Karu Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Kudin Shigar Gwamnatin Sin Ya Karu Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 22, 2026
Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

June 22, 2026
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Dandalin Tattaunawar Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 17

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Dandalin Tattaunawar Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 17

June 22, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Sin Ta Jawo Jarin Waje Yuan Biliyan 327.29 Daga Janairu Zuwa Mayu Na Bana

Sin Ta Jawo Jarin Waje Yuan Biliyan 327.29 Daga Janairu Zuwa Mayu Na Bana

June 22, 2026
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-23 Sun Samu Horaswar Farko Kan Ceto Mara Lafiya A Da’irar Sama

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-23 Sun Samu Horaswar Farko Kan Ceto Mara Lafiya A Da’irar Sama

June 22, 2026
Sin Ta Kara Sassa 10 Na Kasar Amurka Cikin Jerin Bangarorin Da Ta Haramta Fitar Da Hajoji Zuwa Gare Su

Sin Ta Kara Sassa 10 Na Kasar Amurka Cikin Jerin Bangarorin Da Ta Haramta Fitar Da Hajoji Zuwa Gare Su

June 22, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Mataimakin Sakataren Majalisar Koli Ta Tsaron Iran 

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Mataimakin Sakataren Majalisar Koli Ta Tsaron Iran 

June 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.