ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gudanar Da Zauren Tattaunawa Na Ministoci Karo Na Biyu

by Sulaiman
1 year ago
Tarayya

Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ta fara zagaye na biyu na Zauren Tattaunawa na Ministoci, inda Ministan Raya Kiwon Dabbobi, Alhaji Idi Mukhtar; da Ministan Cigaban Yankuna, Injiniya Abubakar Eshiokpekha Momoh, da Ƙaramin Ministan sa, Alhaji Uba Maigari Ahmadu, suka gabatar da jawabai kan ayyukan ma’aikatun su.  

 

Da yake gabatar da jawabin maraba, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana wannan zama da aka yi ranar Juma’a a matsayin dandalin da ke bajekolin nasarorin da Gwamnatin Tinubu ta cimma a fannoni daban-daban.

ADVERTISEMENT
  • KACCIMA Za Ta Baje Kolin Kayan Abincin Azumi Don Saukaka Wa Al’umma – Sidiya Gambo
  • Saudiyya Za Ta Haramta Shan Giya Lokacin Gasar Kofin Duniya

Ya ce: “Ina maku maraba da zuwa zagaye na biyu na Zauren Tattaunawa na Ministoci na shekarar 2025. Kamar yadda kuka sani, a ranar Talata, 11 ga Fabrairu, 2025, na ƙaddamar da wannan jerin tarurruka na bana, inda na jaddada manyan nasarorin da aka cimma a ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.”

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Ya ce Ma’aikatar Raya Kiwon Dabbobi da ta Cigaban Yankuna suna daga cikin sababbin ma’aikatun da Shugaban Ƙasa Tinubu ya ƙirƙira domin bunƙasa fannin kiwo da haɓaka cigaban yankuna a Nijeriya.

 

Ya ce: “Waɗannan ma’aikatun guda biyu su ne sababbi a ƙasar. An kafa Ma’aikatar Raya Kiwon Dabbobi a watan Yulin 2024 domin sauya damar kiwon dabbobi mai darajar biliyoyin daloli zuwa ingantaccen cigaban tattalin arziki ga ‘yan Nijeriya.

 

“Haka nan, an kafa Ma’aikatar Raya Yankuna a watan Oktoban 2024 domin kula da ayyukan hukumomin raya yankuna a faɗin ƙasar nan.

Tarayya

“Tun bayan kafuwar waɗannan ma’aikatun, ministocin sun fara aiki da himma, kuma sun zo a yau domin ƙarin bayani kan abin da suka aiwatar tun daga lokacin da aka ƙirƙiri ma’aikatun nasu.”

 

Ministan ya yaba da rawar da ‘yan jarida ke takawa wajen yaɗa labaran zaman tattaunawar ministocin, yana mai cewa su ne ginshiƙin isar da sahihan bayanai ga ‘yan Nijeriya.

 

Ya kuma buƙaci ‘yan jarida da su guji yaɗa rahotannin da ke da ruɗani ko kwaskwarima.

 

Ya ce: “Kafofin watsa labarai sun kasance abokan hulɗar da ba za a iya musantawa ba a ƙoƙarin mu na ci gaba da sanar da ‘yan Nijeriya kan manyan nasarorin da Gwamnatin Tinubu ta cimma.

 

“Ina kira ga ‘yan jarida da su tabbatar da cewa rahotannin da suka shafi waɗannan tarurruka na bayar da bayanai ana gabatar da su da cikakken adalci da inganci.

 

“Bai kamata a riƙa cusa son rai ko ɓata gaskiya wajen rahoto kan manufofi da shirye-shiryen gwamnati ba.

 

“Yana da kyau a samu sukar ra’ayi da bambancin fahimta domin dimokiraɗiyya, amma kada a bari ji-ta-ji-ta da karkatar da gaskiya su samu gurbi a muhawarar jama’a.”

 

Ya tabbatar da cewa gwamnati za ta yaɗa bayanan wannan zaman tattaunawar ta kafafen yaɗa labarai daban-daban domin tabbatar da gaskiya da karɓar ra’ayoyin jama’a.

 

Za a ci gaba da shirye-shiryen Zauren Tattaunawa na Ministocin, inda manyan jami’an gwamnati za su riƙa gabatar da bayanai kan cigaban da ake samu a fannoni daban-daban.

Tarayya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
  • Sulaiman
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • Sulaiman
    Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita
  • Sulaiman
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci
Labarai

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Labarai

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Next Post
David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa – Amorim

David Moyes Ba Kanwar Lasa Bane A Harkar Ƙwallon Ƙafa - Amorim

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.