• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Natasha Da Akpabio: Sanata Natasha Ta Gabatar Wa Majalisar Dattawa Ƙorafinta

by Sadiq
3 months ago
in Manyan Labarai
0
Natasha Da Akpabio: Sanata Natasha Ta Gabatar Wa Majalisar Dattawa Ƙorafinta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A zaman Majalisar Dattawa na ranar 20 ga Fabrairu, wata sabuwar taƙaddama ta kunno kai tsakanin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, da Sanata Natasha Akpoti Uduaghan mai wakiltar Kogi ta Tsakiya.

Sanata Natasha ta gabatar da ƙorafi kan Akpabio, inda ta zarge shi da cin zarafi da kuma tursasawa wajen hana ta gudanar da aikinta a matsayin ƴar majalisa.

Ta bayyana cewa Shugaban Majalisar ya yi amfani da matsayinsa wajen tauye haƙƙinta da ƙetare iyakarsa.

Yadda Rikicin Ya Faro

Rikicin ya samo asali ne lokacin da mai tsawatarwa na majalisar, Sanata Mohammed Munguno, ya bayyana cewa Sanata Natasha ta ƙi komawa sabuwar kujerar da aka ware mata.

Wannan ya haifar da gagarumin ce-ce-ku-ce har Shugaban Majalisar, Akpabio, ya umarci jami’an tsaro da su fitar da ita daga zauren majalisar.

Labarai Masu Nasaba

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Bayan haka, ƙungiyoyi da jama’a da dama sun buƙaci a yi bincike kan lamarin, wanda ya kai ga Majalisar Dattawa ta buƙaci Sanata Natasha ta bayyana kanta da kuma gabatar da ƙorafi a hukumance.

Sanata Natasha Ta Gabatar Da Ƙorafinta

A ranar Laraba ta gabatar da ƙorafin, Sanata Natasha ta isa majalisar ne tare da mai gidanta, sannan ta yi magana kai-tsaye ga Shugaban Majalisar.

Ta ce: “Ina gabatar da ƙorafi kan Shugaban Majalisar Dattawa, mai girma Sanata Godswill Akpabio, bisa cin zarafi, tursasawa da ƙoƙarin daƙile min aikina a matsayin ƴar majalisa.”

Daga nan, ta sauka daga kujerarta zuwa gaban Akpabio, inda ta rusuna tare da miƙa takardun ƙorafinta.

Martanin Akpabio

Sanata Akpabio ya karɓi ƙorafin Natasha, amma ya yi watsi da zarge-zargen da ta ke masa.

“Na miƙa wannan ƙorafi ga kwamitin ladabtarwa don yin nazari. Amma ina so na fayyace cewa ba ni da wata alaƙa da zargin cin zarafi da aka yi min.”

Ya ci gaba da cewa bai taɓa cin zarafin wata mace ba, yana mai bayyana cewa mahaifiyarsa ta koya masa mutunta mata.

Ya kuma ƙara da cewa yana da ‘ya’ya mata huɗu, don haka ba zai taɓa aikata abin da ake zarginsa da shi ba.

Ƴan Majalisa Ba Su Goyi Bayan Natasha Ba

Duk da cewa Sanata Natasha ta gabatar da ƙorafinta, kusan dukkanin ƴan majalisar da suka yi tsokaci ba su goyi bayan ta ba.

Hatta Sanatoci mata ƴan uwanta ba su mara mata baya.

Wasu sanatocin sun ce irin wannan ƙorafi bai dace a gabatar da shi a majalisa ba, yayin da wasu suka buƙaci a yi ganawar sirri kan batun.

Sai dai Akpabio ya ce hakan ba zai yiwu ba, domin akwai wakilai daga Birtaniya da suka halarci zaman majalisar domin nazarin yadda al’amura ke gudana.

Tuni lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce a cikin majalisa da wajenta,


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cin ZarafiGodswill AkpabioMajalisar DattawaSanata NatashaZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Koya Min Girmama Mata – Akpabio Ya Musanta Zargin Cin Zarafin Natasha

Next Post

Eric Chelle Ya Sake Bai Wa Ahmed Musa Damar Taka Leda A Super Eagles

Related

Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 
Manyan Labarai

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

4 hours ago
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru
Manyan Labarai

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

10 hours ago
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta
Manyan Labarai

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

11 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

1 day ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

2 days ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

2 days ago
Next Post
Shin Ahmed Musa Zai Iya Dawowa Da Rigarsa A Super Eagles Kuwa?

Eric Chelle Ya Sake Bai Wa Ahmed Musa Damar Taka Leda A Super Eagles

LABARAI MASU NASABA

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

Jirgin Sojoji Yayi Kuskuren Buɗe Wuta Kan Ƴan Sa Kai A Maru

June 2, 2025
Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

Ɗaliban Northwest Kano Sun Yi Zanga-Zanga Kan Ƙarin Kuɗin Makaranta

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.