ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Natasha Da Akpabio: Sanata Natasha Ta Gabatar Wa Majalisar Dattawa Ƙorafinta

by Sadiq
1 year ago
Natasha

A zaman Majalisar Dattawa na ranar 20 ga Fabrairu, wata sabuwar taƙaddama ta kunno kai tsakanin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, da Sanata Natasha Akpoti Uduaghan mai wakiltar Kogi ta Tsakiya.

Sanata Natasha ta gabatar da ƙorafi kan Akpabio, inda ta zarge shi da cin zarafi da kuma tursasawa wajen hana ta gudanar da aikinta a matsayin ƴar majalisa.

Ta bayyana cewa Shugaban Majalisar ya yi amfani da matsayinsa wajen tauye haƙƙinta da ƙetare iyakarsa.

ADVERTISEMENT

Yadda Rikicin Ya Faro

Rikicin ya samo asali ne lokacin da mai tsawatarwa na majalisar, Sanata Mohammed Munguno, ya bayyana cewa Sanata Natasha ta ƙi komawa sabuwar kujerar da aka ware mata.

Wannan ya haifar da gagarumin ce-ce-ku-ce har Shugaban Majalisar, Akpabio, ya umarci jami’an tsaro da su fitar da ita daga zauren majalisar.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Bayan haka, ƙungiyoyi da jama’a da dama sun buƙaci a yi bincike kan lamarin, wanda ya kai ga Majalisar Dattawa ta buƙaci Sanata Natasha ta bayyana kanta da kuma gabatar da ƙorafi a hukumance.

Sanata Natasha Ta Gabatar Da Ƙorafinta

A ranar Laraba ta gabatar da ƙorafin, Sanata Natasha ta isa majalisar ne tare da mai gidanta, sannan ta yi magana kai-tsaye ga Shugaban Majalisar.

Ta ce: “Ina gabatar da ƙorafi kan Shugaban Majalisar Dattawa, mai girma Sanata Godswill Akpabio, bisa cin zarafi, tursasawa da ƙoƙarin daƙile min aikina a matsayin ƴar majalisa.”

Daga nan, ta sauka daga kujerarta zuwa gaban Akpabio, inda ta rusuna tare da miƙa takardun ƙorafinta.

Martanin Akpabio

Sanata Akpabio ya karɓi ƙorafin Natasha, amma ya yi watsi da zarge-zargen da ta ke masa.

“Na miƙa wannan ƙorafi ga kwamitin ladabtarwa don yin nazari. Amma ina so na fayyace cewa ba ni da wata alaƙa da zargin cin zarafi da aka yi min.”

Ya ci gaba da cewa bai taɓa cin zarafin wata mace ba, yana mai bayyana cewa mahaifiyarsa ta koya masa mutunta mata.

Ya kuma ƙara da cewa yana da ‘ya’ya mata huɗu, don haka ba zai taɓa aikata abin da ake zarginsa da shi ba.

Ƴan Majalisa Ba Su Goyi Bayan Natasha Ba

Duk da cewa Sanata Natasha ta gabatar da ƙorafinta, kusan dukkanin ƴan majalisar da suka yi tsokaci ba su goyi bayan ta ba.

Hatta Sanatoci mata ƴan uwanta ba su mara mata baya.

Wasu sanatocin sun ce irin wannan ƙorafi bai dace a gabatar da shi a majalisa ba, yayin da wasu suka buƙaci a yi ganawar sirri kan batun.

Sai dai Akpabio ya ce hakan ba zai yiwu ba, domin akwai wakilai daga Birtaniya da suka halarci zaman majalisar domin nazarin yadda al’amura ke gudana.

Tuni lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce a cikin majalisa da wajenta,

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Shin Ahmed Musa Zai Iya Dawowa Da Rigarsa A Super Eagles Kuwa?

Eric Chelle Ya Sake Bai Wa Ahmed Musa Damar Taka Leda A Super Eagles

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.