• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Ma’aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aikin hukumar bunkasa noman kwakwa ta Legas ce ta taimaka wajen bunkasa harkar ta yadda za a dinga samar da ita sosai ga kasuwa.

Shugaban hukumar Dapo Olakulehin ya ce jihar ita ce kan gaba wajen samar da kwakwa a kasar nan, inda ya kara da cewa, amma ba a iya wadata kasar da ita saboda karuwar masu sarrafa ta a cikin shekara 10 zuwa 15 da suka wuce.

  • Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Gudanar Da Aikin Tsabtace Muhalli A Maiduguri
  • “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

Olakulehin ya ci gaba da cewa, a shekara uku da suka wuce, lokacin da muka ga alamar karuwar bukatarta, sai muka dinga karfafa wa mutane gwiwa kan su shiga harkar domin samar da ita yadda ake bukata.

A shekara hudu zuwa biyar masu zuwa za a fara ganin tasirin hakan idan bishiyoyin suka fara ‘ya’ya, inda ya ce hukumar bunkasa noman kwakwar ta Legas tana da fili, inda take samar da dashen itaciyar da take raba wa jama’a.

Shugaban ci gaba da cewa, a bara ta raba wa manoma har dashe dubu 200 kyauta, amma duk da haka ba su isa ba, inda ya sanar da cewa, a bana kuwa dashe dubu 80 kawai hukumar ta iya raba wa, wanda wannan na nufin masu sarrafa kwakwar a Nijeriya dole ne su ci gaba da sayo ta daga waje kafin wani lokaci nan gaba.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Shi kuwa wani babban jami’i a Ma’aikatar Masana’antu da kasuwanci da zuba jari ta kasa Kaura Arimiye, cewa ya yi gwamnati ta dauki wannan harka a matsayin wata hanya ta rage yawan marasa aikin yi da kuma rage dogaron da kasar ke yi a kan man fetur domin samun kudi daga kasar waje.

Wata mai kamfanin sarrafa kwakwar, wajen yin abubuwa daban-daban Ebun Feludu, ta ce, tana ganin idan gwamnati na son cim ma bukatar hakan to sai ta bunkasa muhimman abubuwan inganta rayuwa kamar wutar lantarki da tituna da sauransu.

Ta ce Nijeriya ta yi kaurin suna wajen rashin wutar lantarki, haka ma tituna ba su da kyau, inda ta kara da cewa, akwai bukatar gwamnatin ta rage hidima da kudin fitar da kayan zuwa kasuwannin duniya.

Shugabar kungiyar manoma da masu sarrafawa da sayar da kwakwar na kasa Nma Okoroji, ta ce mutane na kara samun wayewa da fahimtar cewa harka ce ta samun kudi.

Nma ta ci gaba da cewa, kwakwa za ta iya kara yawan kudin da Nijeriya ke samu, inda ta bayyana cewa, muna da kyakkyawan yanayi da filin nomanta da kuma manoman, da su yi ta.

Ta ce, muna ma fitar da ita kasashe maimakon mu sayo daga ketare, inda ta kara da cewa, mutane da yawa a Afirka ta Yamma na ci da shan ruwan kwakwa.

Ta kara da cewa , aiki karkashin wani shiri na bunkasa samar da kwakwar a kasar nan, tare da tallafin gwamnati, inda ta sanar da cewa, shirin da a karkashinsa ake kudurin dasa itatuwan kwakwa a fili mai girman hekta 10,000 a yawancin jihohin Nijeriya 36 zuwa shekara ta 2027.

Ta sanar da cewa, sai dai babbar matsalar ita ce ta samun ingantaccen irin kwakwar, inda ta ci gaba da cewa, iri ma fi inganci shi ne na aure wanda aka samar daga, hadin doguwar bishiyar kwakwar ta Afirka ta Yamma da kuma gajeruwa ta yankin Asiya.

Ta bayyana cewa, shekara hudu zuwa biyar, ba kamar gajeruwa ta Asia ba, wadda take fara ‘ya’ya a cikin shekara biyu da rabi zuwa uku, inda ta ce amma kuma ita ta aure kwararru sun samar da ita ne musamman domin noma na kasuwanci.

Shi ma wani da ke a cikin fannin mai suna Abiodun Oyelekan, ya ce yana da kyau a yi amfani da kwakwar ‘yar aure saboda yawan ‘ya’yan da take samarwa a shekara.

Ya sanar da cewa, amma tana da tsada domin duk dashe daya ya kai kusan dala shida wanda hakan ya sa ta fi karfin yawancin kananan manoman da ke a cikin fannin a kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DapoKwakwaNomaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bullar Sabuwar Cuta: Manoman Dankalin Turawa Sun Karaya

Next Post

RTEAN Za Ta Jagoranci Samar Da Motoci Masu Amfani Da Iskar Gas A Nijeriya

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

23 hours ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

1 day ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

2 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

2 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

3 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

3 weeks ago
Next Post
RTEAN Za Ta Jagoranci Samar Da Motoci Masu Amfani Da Iskar Gas A Nijeriya

RTEAN Za Ta Jagoranci Samar Da Motoci Masu Amfani Da Iskar Gas A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

September 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

September 7, 2025
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.