• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Al’ummar Kasar Sin Ke Tabbatar Da Hakkinsu Na Demokuradiyya 

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Al’ummar Kasar Sin Ke Tabbatar Da Hakkinsu Na Demokuradiyya 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kauyen Gulu, mazauna kauyen suna tattaunawa kan bukatunsu, inda malam Shen Shaohua ya ce, “Akwai mutane 6 a gidana, shi ya sa muna bukatar sassan da abin ya shafa su kara inganta manufar inshorar lafiyar mazauna kauyuka.” malam Zheng Wangchun mai shekaru 37 a duniya, ya kuma rubuta bukatun Shen da na sauran mazauna kauyen bi da bi. 

Kauyen Gulu kauye ne na ‘yan kabilar Yi, wanda ke can karkarar lardin Sichuan da ke kudu maso yammacin kasar Sin, kuma malam Zheng Wangchun haifaffen kauyen ne, wanda a shekarar 2023, aka zabe shi a matsayin dan majalisar wakilan jama’ar kasar Sin. Tun lokacin kuma, kullum ya kan tattauna da magidanta fiye da 200 na kauyen.

  • Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Kano, Sun Sace Mutum Ɗaya
  • An Rufe Taro Na 3 Na Majalisar CPPCC Karo Na 14

Bayan tattaunawa da ya yi da mazauna kauyen, Zheng ya fahimci cewa, yawan kudin da aka biya ya karu a kowace shekara duba da kyautatuwar tsarin inshorar lafiya na Sin, sai dai ba abu mai sauki ba ne ga mazauna kauyen kamar Shen Shaohua mai mambobin iyali da yawa su biya kudaden. Amma idan ba su shiga inshorar ba, ya yiwu su koma talauci idan rashin lafiya mai tsanani ya same su. Hakan ya sa a taron shekara shekara na majalisar wakilan jama’ar Sin da ke gudana a kwanakin nan a birnin Beijing, Zheng ya hallara tare da gabatar da shirin da ya shafi rage yawan kudaden da jama’a za su biya kan inshorar lafiya, da habaka amfanin inshorar ga karin mutane.

Alkaluman da aka samar sun shaida cewa, sassan majalisar gudanarwar kasar Sin sun daidaita irin shirye-shiryen 8783 kan lokaci a bara, wanda ya kai kashi 95.1% da dukkanin shirye-shiryen da ‘yan majalisar wakilan jama’ar kasar suka gabatar. Wadannan shirye-shirye masu dauke da burin jama’a kamar na mazauna kauyen Gulu, wata muhimmiyar hanya ce ta tattara ra’ayi da basirar jama’a.

A nan kasar Sin, yawan ‘yan majalisar wakilan jama’ar kasar Sin irinsa Zheng Wangchun ya kai kusan 3000, wadanda suka fito daga wurare, kabilu ko sana’o’i daban-daban, wadanda kuma suka kasance mahada dake sada tsakanin jama’a da gwamnatin. Matsayinsu na tabbatar da ana jin muryoyin jama’a duk inda suka fito. Wannan shi ne tsarin majalisar wakilan jama’ar Sin, hanyar da jama’ar kasar ke sa hannu cikin harkokin kasar don tabbatar da hakkin jama’a a cikin zaman rayuwarsu a bangaren demokuradiyya. (Mai zane da rubutu: MINA)

Labarai Masu Nasaba

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Miƙawa Gwamnatin Borno Mutane 75 Da Suka Ceto

Next Post

Tambuwal Ya Tallafawa Magidanta Dubu 30 Da Kayan Abinci

Related

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

8 hours ago
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan
Daga Birnin Sin

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

9 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

10 hours ago
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

11 hours ago
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

12 hours ago
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”
Daga Birnin Sin

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

13 hours ago
Next Post
Tambuwal Ya Tallafawa Magidanta Dubu 30 Da Kayan Abinci

Tambuwal Ya Tallafawa Magidanta Dubu 30 Da Kayan Abinci

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Sin

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.