• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sabunta Kayan Aikin Gidajen Watsa Labarai, In Ji Minista

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sabunta Kayan Aikin Gidajen Watsa Labarai, In Ji Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta fara zuba jari wajen samar da sababbin fasahohi da na’urorin zamani domin ƙarfafa ayyukan kafafen yaɗa labarai na gwamnati.

 

Ya bayyana hakan ne a birnin Las Vegas da ke Jihar Nevada ta ƙasar Amurka yayin wata tattaunawa da manyan kamfanonin watsa shirye-shirye a taron Ƙungiyar Ƙasa ta Masu Watsa Shirye-shirye (NAB) 2025 da aka gudanar.

  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China
  • Gwamna Lawal Ya Yi Jimamin Rasuwar Ɗan Majalisar Zamfara, Aminu K/Daji

Ya ce wannan zuba jarin zai taimaka wajen sabunta da kuma maye gurbin tsofaffin kayan aiki a tashoshin rediyo da talabijin na Gwamnatin Tarayya.

 

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Domin cimma wannan buri, ministan ya bayyana cewa ma’aikatar sa tana haɗin gwiwa da masana’antun kayan watsa shirye-shirye domin bai wa ‘yan jarida a cikin gida damar cin gajiyar sababbin fasahohi da horo na musamman da ya shafi sana’ar su.

 

Ministan ya jaddada ƙudirin Gwamnati na yin aiki tare da muhimman abokan hulɗa a fannin watsa labarai da sadarwa a duniya domin ƙarfafa tsarin yaɗa labarai a Nijeriya.

 

Ya ce: “Sadarwa na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da cewa manufofin Ajandar Sabunta Fata sun isa ga al’ummar Nijeriya yadda ya kamata.”

 

A yayin taron, Minista ya kai ziyara wuraren da ake baje-kolin kayayyakin zamani da suka haɗa da eriyoyi, na’urorin aika sigina (tiransimita), da kayan aikin situdiyo – duk waɗanda ke da matuƙar muhimmanci wajen inganta watsa shirye-shirye.

 

Waɗansu daga cikin shugabannin kamfanonin da suka gana da ministan sun haɗa da Shugaban KINTRONIC Laboratories, Thomas King; da Shugaban Axel Technology SRL, Enrico Vaccari; da Shugaban SYES SRL, Gianluca Baccalini; da Shugaban Kintronic Labs Inc, Josh King; Shugaban Thomson Broadcast, Khiran Keerodhur, da Shugaban Continental Electronics, Calvin Carter.

 

Dukkan su sun nuna a shirye suke su haɗa gwiwa da Gwamnatin Tarayya domin haɓaka harkar watsa labarai da kuma ƙarfafa hukumomin da ke da alhakin tsarawa da sa ido.

 

A tawagar da Idris ya jagoranta zuwa Amurka ɗin akwai manyan jami’an hukumomin yaɗa labarai na Nijeriya da suka haɗa da Darakta-Janar na NTA, Salihu Abdulhamid Dembos; Manajan-Daraktan Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), Ali Muhammad Ali; Darakta-Janar na Hukumar Kula da Tashoshin Rediyo da Talbijin (NBC), Charles Ebuebu; Shugaban Hukumar Kula da Harkar Tallace-Tallace ta Ƙasa, (ARCON), Dakta Lekan Fadolapo; da Darakta-Janar na tashar Muryar Nijeriya (VON), Jibrin Baba Ndace.

 

Taron na NAB, wanda aka gudanar daga ranakun 5 zuwa 9 ga Afrilu, 2025, yana da taken, “Fasaha, Salo da Makoma”, inda aka tattauna batutuwan zamani kamar Ƙirƙirarriyar Basira (AI), bayyanar bayanai ta hanyar fasahar girgije, tattalin arzikin masu ƙirƙira, da kuma samar da shirye-shiryen wasanni da watsa su ta intanet.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kaddamar Da Bikin Nuna Fina-Finan Sinanci Na CMG Karo Na 5

Next Post

Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

12 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

13 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

15 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

18 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

20 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

21 hours ago
Next Post
Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.