ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sabunta Kayan Aikin Gidajen Watsa Labarai, In Ji Minista

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta fara zuba jari wajen samar da sababbin fasahohi da na’urorin zamani domin ƙarfafa ayyukan kafafen yaɗa labarai na gwamnati.

 

Ya bayyana hakan ne a birnin Las Vegas da ke Jihar Nevada ta ƙasar Amurka yayin wata tattaunawa da manyan kamfanonin watsa shirye-shirye a taron Ƙungiyar Ƙasa ta Masu Watsa Shirye-shirye (NAB) 2025 da aka gudanar.

ADVERTISEMENT
  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China
  • Gwamna Lawal Ya Yi Jimamin Rasuwar Ɗan Majalisar Zamfara, Aminu K/Daji

Ya ce wannan zuba jarin zai taimaka wajen sabunta da kuma maye gurbin tsofaffin kayan aiki a tashoshin rediyo da talabijin na Gwamnatin Tarayya.

 

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Domin cimma wannan buri, ministan ya bayyana cewa ma’aikatar sa tana haɗin gwiwa da masana’antun kayan watsa shirye-shirye domin bai wa ‘yan jarida a cikin gida damar cin gajiyar sababbin fasahohi da horo na musamman da ya shafi sana’ar su.

 

Ministan ya jaddada ƙudirin Gwamnati na yin aiki tare da muhimman abokan hulɗa a fannin watsa labarai da sadarwa a duniya domin ƙarfafa tsarin yaɗa labarai a Nijeriya.

 

Ya ce: “Sadarwa na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da cewa manufofin Ajandar Sabunta Fata sun isa ga al’ummar Nijeriya yadda ya kamata.”

 

A yayin taron, Minista ya kai ziyara wuraren da ake baje-kolin kayayyakin zamani da suka haɗa da eriyoyi, na’urorin aika sigina (tiransimita), da kayan aikin situdiyo – duk waɗanda ke da matuƙar muhimmanci wajen inganta watsa shirye-shirye.

 

Waɗansu daga cikin shugabannin kamfanonin da suka gana da ministan sun haɗa da Shugaban KINTRONIC Laboratories, Thomas King; da Shugaban Axel Technology SRL, Enrico Vaccari; da Shugaban SYES SRL, Gianluca Baccalini; da Shugaban Kintronic Labs Inc, Josh King; Shugaban Thomson Broadcast, Khiran Keerodhur, da Shugaban Continental Electronics, Calvin Carter.

 

Dukkan su sun nuna a shirye suke su haɗa gwiwa da Gwamnatin Tarayya domin haɓaka harkar watsa labarai da kuma ƙarfafa hukumomin da ke da alhakin tsarawa da sa ido.

 

A tawagar da Idris ya jagoranta zuwa Amurka ɗin akwai manyan jami’an hukumomin yaɗa labarai na Nijeriya da suka haɗa da Darakta-Janar na NTA, Salihu Abdulhamid Dembos; Manajan-Daraktan Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), Ali Muhammad Ali; Darakta-Janar na Hukumar Kula da Tashoshin Rediyo da Talbijin (NBC), Charles Ebuebu; Shugaban Hukumar Kula da Harkar Tallace-Tallace ta Ƙasa, (ARCON), Dakta Lekan Fadolapo; da Darakta-Janar na tashar Muryar Nijeriya (VON), Jibrin Baba Ndace.

 

Taron na NAB, wanda aka gudanar daga ranakun 5 zuwa 9 ga Afrilu, 2025, yana da taken, “Fasaha, Salo da Makoma”, inda aka tattauna batutuwan zamani kamar Ƙirƙirarriyar Basira (AI), bayyanar bayanai ta hanyar fasahar girgije, tattalin arzikin masu ƙirƙira, da kuma samar da shirye-shiryen wasanni da watsa su ta intanet.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas
  • Sulaiman
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.