ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sabunta Kayan Aikin Gidajen Watsa Labarai, In Ji Minista

by Sulaiman
1 year ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta fara zuba jari wajen samar da sababbin fasahohi da na’urorin zamani domin ƙarfafa ayyukan kafafen yaɗa labarai na gwamnati.

 

Ya bayyana hakan ne a birnin Las Vegas da ke Jihar Nevada ta ƙasar Amurka yayin wata tattaunawa da manyan kamfanonin watsa shirye-shirye a taron Ƙungiyar Ƙasa ta Masu Watsa Shirye-shirye (NAB) 2025 da aka gudanar.

ADVERTISEMENT
  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China
  • Gwamna Lawal Ya Yi Jimamin Rasuwar Ɗan Majalisar Zamfara, Aminu K/Daji

Ya ce wannan zuba jarin zai taimaka wajen sabunta da kuma maye gurbin tsofaffin kayan aiki a tashoshin rediyo da talabijin na Gwamnatin Tarayya.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Domin cimma wannan buri, ministan ya bayyana cewa ma’aikatar sa tana haɗin gwiwa da masana’antun kayan watsa shirye-shirye domin bai wa ‘yan jarida a cikin gida damar cin gajiyar sababbin fasahohi da horo na musamman da ya shafi sana’ar su.

 

Ministan ya jaddada ƙudirin Gwamnati na yin aiki tare da muhimman abokan hulɗa a fannin watsa labarai da sadarwa a duniya domin ƙarfafa tsarin yaɗa labarai a Nijeriya.

 

Ya ce: “Sadarwa na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da cewa manufofin Ajandar Sabunta Fata sun isa ga al’ummar Nijeriya yadda ya kamata.”

 

A yayin taron, Minista ya kai ziyara wuraren da ake baje-kolin kayayyakin zamani da suka haɗa da eriyoyi, na’urorin aika sigina (tiransimita), da kayan aikin situdiyo – duk waɗanda ke da matuƙar muhimmanci wajen inganta watsa shirye-shirye.

 

Waɗansu daga cikin shugabannin kamfanonin da suka gana da ministan sun haɗa da Shugaban KINTRONIC Laboratories, Thomas King; da Shugaban Axel Technology SRL, Enrico Vaccari; da Shugaban SYES SRL, Gianluca Baccalini; da Shugaban Kintronic Labs Inc, Josh King; Shugaban Thomson Broadcast, Khiran Keerodhur, da Shugaban Continental Electronics, Calvin Carter.

 

Dukkan su sun nuna a shirye suke su haɗa gwiwa da Gwamnatin Tarayya domin haɓaka harkar watsa labarai da kuma ƙarfafa hukumomin da ke da alhakin tsarawa da sa ido.

 

A tawagar da Idris ya jagoranta zuwa Amurka ɗin akwai manyan jami’an hukumomin yaɗa labarai na Nijeriya da suka haɗa da Darakta-Janar na NTA, Salihu Abdulhamid Dembos; Manajan-Daraktan Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), Ali Muhammad Ali; Darakta-Janar na Hukumar Kula da Tashoshin Rediyo da Talbijin (NBC), Charles Ebuebu; Shugaban Hukumar Kula da Harkar Tallace-Tallace ta Ƙasa, (ARCON), Dakta Lekan Fadolapo; da Darakta-Janar na tashar Muryar Nijeriya (VON), Jibrin Baba Ndace.

 

Taron na NAB, wanda aka gudanar daga ranakun 5 zuwa 9 ga Afrilu, 2025, yana da taken, “Fasaha, Salo da Makoma”, inda aka tattauna batutuwan zamani kamar Ƙirƙirarriyar Basira (AI), bayyanar bayanai ta hanyar fasahar girgije, tattalin arzikin masu ƙirƙira, da kuma samar da shirye-shiryen wasanni da watsa su ta intanet.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

Karin Harajin Amurka: Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.