• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CITAD Ta Bai Wa ‘Yan Jarida 10 Tallafi Don Gudanar Da Bincike Game Da Cin Hanci

by Sadiq
3 years ago
CITAD

Akalla ‘yan jarida 10 ne suka samu tallafin kudi don gudanar da bincike kan cin hanci da rashawa a tsakanin al’umma.

Cibiyar Fasaha da Ci Gaban Al’umma (CITAD) ce ta ba da tallafin tare da hadin gwiwar gidauniyar MacArthur.

  • Miyetti Allah Ta Maka Gwamna Ortom A Kotu Kan Kwace Wuraren Yin Kiwo A Jihar Benuwai
  • Daga Soyayyar Wata Yarinya Na Fara Waka —Abba Ganga

Babban Daraktan Cibiyar, Malam Yunusa Ya’u, wanda Buhari Abba ya wakilta, ya bayyana cewa tun farkon watan Yuni, CITAD ta bukaci ‘yan jarida da suka halarci taron bita na kwana biyu a jihar Bauchi, kan karamin tallafin bincike na yaki da cin hanci da rashawa.

Akalla mutane 15 ne suka shiga takarar neman tallafin.

Bayan da alkalai da masu ruwa da tsaki suka tantance, sun zabo ‘yan jarida 10 don ba su tallafin da za su yi amfani da shi wajen gudanar da bincike.

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Babban Darakta na CITAD, Injiniya Y. Z. Ya’u, ya ce, tallafin wani hadin guiwa ne Gidauniyar Macarthur don bai wa ’yan jarida kwarin guiwa wajen yin bincike da kuma bayar da rahoton ayyukan cin hanci da rashawa a cikin al’umma ta hanyar jan hankalin gwamnati da masu ruwa da tsaki don yin gyara.

“CITAD ta dade tana aiki tare da ‘yan jarida don tabbatar da gaskiya da rikon amana a tsakanin jama’a kuma wannan tallafin zai zama na musamman duba da yanayin wadanda zasu yi binciken matasa ne masu sha’awar kawo canji a cikin al’umma.”

“Binciken ayyukan cin hanci da rashawa a cikin cibiyoyin gwamnati da masu zaman kansu zai inganta rayuwar jama’a musamman a cikin al’ummomin da ba su da murya don yaki da cin hancin.”

Wadanda suka yi nasara sun fito ne daga kafofin yada labarai daban-daban wadanda suka hada da:

1 – Auta Polycarp – Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN).

2 – Ismail Auwal Garba – Sahelian Times.

3 – Edwin Philip – Breeze FM Lafia, Nasarawa.

4 – Anibe Idajili – TheCable.

5 – Hauwa Kabir Lawal – Daily Reality Newspaper, Jihar Filato.

6 – Abbakar Muhammad Usman – Daily Trust.

7 – Rabiu Musa – Hot Pen, Kano.

8 – Abdulhafiz Sultan – Jasawa Times, Jihar Filato.

9 – Muhammad Auwal Ibrahim – Wikki Times, Jihar Gombe.

10 – Zaharaddeen S. Yakubu – Daily Trust, Jihar Kano.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Next Post
Sin: Cinikin Kayayyakin Abinci Zai Kara Amfanawa Jama’ar Sin Da Afirka

Sin: Cinikin Kayayyakin Abinci Zai Kara Amfanawa Jama'ar Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

October 16, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.