ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CITAD Ta Bai Wa ‘Yan Jarida 10 Tallafi Don Gudanar Da Bincike Game Da Cin Hanci

by Sadiq
4 years ago
CITAD

Akalla ‘yan jarida 10 ne suka samu tallafin kudi don gudanar da bincike kan cin hanci da rashawa a tsakanin al’umma.

Cibiyar Fasaha da Ci Gaban Al’umma (CITAD) ce ta ba da tallafin tare da hadin gwiwar gidauniyar MacArthur.

  • Miyetti Allah Ta Maka Gwamna Ortom A Kotu Kan Kwace Wuraren Yin Kiwo A Jihar Benuwai
  • Daga Soyayyar Wata Yarinya Na Fara Waka —Abba Ganga

Babban Daraktan Cibiyar, Malam Yunusa Ya’u, wanda Buhari Abba ya wakilta, ya bayyana cewa tun farkon watan Yuni, CITAD ta bukaci ‘yan jarida da suka halarci taron bita na kwana biyu a jihar Bauchi, kan karamin tallafin bincike na yaki da cin hanci da rashawa.

ADVERTISEMENT

Akalla mutane 15 ne suka shiga takarar neman tallafin.

Bayan da alkalai da masu ruwa da tsaki suka tantance, sun zabo ‘yan jarida 10 don ba su tallafin da za su yi amfani da shi wajen gudanar da bincike.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Babban Darakta na CITAD, Injiniya Y. Z. Ya’u, ya ce, tallafin wani hadin guiwa ne Gidauniyar Macarthur don bai wa ’yan jarida kwarin guiwa wajen yin bincike da kuma bayar da rahoton ayyukan cin hanci da rashawa a cikin al’umma ta hanyar jan hankalin gwamnati da masu ruwa da tsaki don yin gyara.

“CITAD ta dade tana aiki tare da ‘yan jarida don tabbatar da gaskiya da rikon amana a tsakanin jama’a kuma wannan tallafin zai zama na musamman duba da yanayin wadanda zasu yi binciken matasa ne masu sha’awar kawo canji a cikin al’umma.”

“Binciken ayyukan cin hanci da rashawa a cikin cibiyoyin gwamnati da masu zaman kansu zai inganta rayuwar jama’a musamman a cikin al’ummomin da ba su da murya don yaki da cin hancin.”

Wadanda suka yi nasara sun fito ne daga kafofin yada labarai daban-daban wadanda suka hada da:

1 – Auta Polycarp – Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN).

2 – Ismail Auwal Garba – Sahelian Times.

3 – Edwin Philip – Breeze FM Lafia, Nasarawa.

4 – Anibe Idajili – TheCable.

5 – Hauwa Kabir Lawal – Daily Reality Newspaper, Jihar Filato.

6 – Abbakar Muhammad Usman – Daily Trust.

7 – Rabiu Musa – Hot Pen, Kano.

8 – Abdulhafiz Sultan – Jasawa Times, Jihar Filato.

9 – Muhammad Auwal Ibrahim – Wikki Times, Jihar Gombe.

10 – Zaharaddeen S. Yakubu – Daily Trust, Jihar Kano.

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Sin: Cinikin Kayayyakin Abinci Zai Kara Amfanawa Jama’ar Sin Da Afirka

Sin: Cinikin Kayayyakin Abinci Zai Kara Amfanawa Jama'ar Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.