• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

by Abubakar Abba
5 months ago
in Tattalin Arziki
0
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, ta bukaci ‘yan kasuwa da sauran alummar kasar nan, da su yi amfani da damar hanyoyin sauki da Hukumar ta samar wajen fitar da kaya zuwa kasar waje

Shugabanta, Dakta Abubakar Dantsoho ne, ya yi wannan kiran a cikin sanawar da Hukumar ta fitar a yayin taron baje koli karo na 36 da ta baje koli ta hada-hadar kasuwanci, masana’antu da kuma aikin noma ta jihar Enugu, ta shirya.

  • Kwararru Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Dangane Da Wayewar Kan Sin Da Afirka 
  • Yadda Hukuncin Kotun Koli Ya Kara Dagula Rikicin Shugabanci A PDP Da LP

“Daga cikin kokarin Hukumar na kara karfafa kasuwanici a cikin gida Nijeriya NPA ta hanyar amfani da daukaka kasuwanci, ta kafa sashen da ke samar wa masu son fiton kaya zuwa kasar waje, a cikin sauki”.

Kazalika, Dantsoho ya jaddada cewa, Hukumars, ta samar da matakan da za ta sada masu hada-hadar kasuwanci da gureren da ke wuyar shigar da kayan da musamman ake da bukatar su, a fadin duniya.

Dantsoho ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA, ako wanne lokaci tana tunkaho da Cibiyar da baje kolin ta jihar Enugu, musamman duba da cewa, gudanar da hada-hadar kasuwanci shi ne, kashin bayan bunkasa tattalin arziki.

Labarai Masu Nasaba

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

Shugaban ya kuma bai wa masu ruwa da tsaki a fannin cewa, ako da yaushe, kofar Hukumar ta NPA, bode take domin hadaka wacce ta zarce ta gudanar da baje koli.

Dakta Dantsoho ya kara da cewa, an samar da tsarin na EPT domin a tabbatar da cewa, ana fitar da kaya zuwa waje, ta hanyar yin amfani da na’urar zamani.

“Wannan na zai taimaka matuka wajen kaucewa samun jinkiri da kuma mai-maita aiki da Hukumar ta saba fuskanta a baya,” A cewar Dantsoho.

Kazalika, Dantsoho ya bayyana cewa, domin a samu sauki wajen kai kaya a tsakanin masu kananan da matsakaitan sana’oi, musamman duba da cewa, tsarin na EPT, zai taimaka matuka ga guraren da ake adana kaya a cikin kasar na, da kuma hada karfi da karfe da Hukumar Bunkasa Harkokin Fitar da Kayayyaki ta Kasa NEPC da sauran abokan hadaka.

“Domin Hukumar ta NPA ta gudnar da ayyukanta daidai da tsarin Gwamnatin Tarayya na samar da sauki ga yin kasuwanci, musamman duba da taken baje kolin na ta baje koli ta hada-hadar kasuwanci, masana’antu da kuma aikin noma ta jihar Enugu, Hukumar NPA ta samar da tsarin samar da sauki wajen bai wa ‘yan kasuwar kasar yadda za su rinka fitar da kayansu, zuwa ketare,”. Inji Dantsoho.

Shugaban ya kara da cewa, Hukumar ta kuma nasara a tsarinta na NSW, musamman duba da yadda aka samu saduwa da sauran masu ruwa da tsaki, wajen gudanar da hada-hadar kasuwanci

Dantsoho ya jinjinawa mahukunta Cibiyar ta baje koli ta hada-hadar kasuwanci, masana’antu da kuma aikin noma ta jihar Enugu, musamman kan yadda suke ci gaba da gudanar da hada-hara kasuwanci da yanyo abokan kasuwanci na cikin gida Nijeriya, da kuma na kasashen waje, wanda hakan ya kara taimakawa, wajen habaka tattalin arzikin kasar.

Shugaban ya yi nuni da cewa, duba da yadda jihar ta Enugu ta kasance a yankin Kudu Maso Gabas, hakan zai taimaka mata wajen samar da damar kara fadada fitar da kaya zuwa ketare.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DantsohoKayaNPA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

Next Post

China Na Neman Ƙasashe Su  Haɗe Wa Amurka Kai Sakamakon Ƙarin Haraji

Related

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

6 days ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

2 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

2 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

2 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

3 weeks ago
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku
Tattalin Arziki

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

3 weeks ago
Next Post
China Na Neman Ƙasashe Su  Haɗe Wa Amurka Kai Sakamakon Ƙarin Haraji

China Na Neman Ƙasashe Su  Haɗe Wa Amurka Kai Sakamakon Ƙarin Haraji

LABARAI MASU NASABA

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.