ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

China Na Neman Ƙasashe Su  Haɗe Wa Amurka Kai Sakamakon Ƙarin Haraji

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
China

Jakadan ƙasar China a Nijeriya, Yu Dunhai, ya yi kira ga al’ummar duniya da su haɗa kai don yaƙi da yawan haraji da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ke ƙara wa ƙasashe da dama, yana gargadin cewa wannan mataki na iya janyo koma baya ga tattalin arziƙin duniya tare da illoli masu tsanani musamman ga Afrika.

A lokacin taron manema labarai da ya yi a Abuja ranar Juma’a, jakadan ya jaddada cewa matakan Amurka sun take haƙƙin ƙasashe da dama, sun saɓa dokokin yarjejeniyar kasuwanci ta duniya (WTO), suna kuma kawo matsala ga tsarin ciniki na ƙasa da ƙasa da zai iya haifar da rushewar tsarin tattalin arzikin duniya.

  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China
  • EFCC Ta Gurfanar Da Ɗan China A Kotu Kan Bayar Da Bayanan Ƙarya

Ya bayyana cewa, “Al’ummar duniya dole ne su haɗa kai su yaƙi wannan zalunci domin kare abubuwan da suka shafi al’umma baki ɗaya. Ya ƙalubalanci amfani da haraji a matsayin abin cin fuska ko tirsasawa daga Amurka da nufin tsayawa kan daidaito da gaskiya da kuma adalci.”

Shugaban Amurka ya ƙara tsananta haraji ga ƙasashe da dama, China tana cikin waɗanda suka fi fuskantar ƙarin haraji mai yawa, da 145% na kayan China da sazu shiga kasuwar Amurka, yayin da Beijing ta mayar da martani da haraji na 125% kan kayan Amurka.

ADVERTISEMENT

Ƙasashe da dama ciki har da Tarayyar Turai (EU) sun ɗora haraji a kan Amurka, wanda ya sa gwamnatin Trump ta dakatar da aiwatar da sabon tsarin haraji na kwanaki 90 domin buɗe damar tattaunawa.

Jakada Dunhai ya ƙara da cewa wannan tsarin haraji yana keta ƙa’idar tattalin arziƙi da dokokin kasuwanci, da ƙin la’akari da cewa Amurka ta daɗe tana cin riba daga kasuwanci na ƙasa da ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

“Amfani da haraji a matsayin makami don matsin lamba da son rai yana nuni da tsarin siyasa na rashin haɗin kai da kare tattalin arziƙi da kuma zambar tattalin arziƙi. Wannan ba abu ne na adalci ba ko mai kyau – yana nufin zaman ‘Amurka da tafi kowa’ da kuma ƙaruwar ƙarfin Amurka,” in ji shi.

Jakadan ya kuma yi gargadi cewa ƙasashe masu tasowa za su fi shan wahala daga wannan tsarin haraji, kuma hakan zai fi cutar da ƙasashen Afrika, ciki har da Nijeriya.

Ya bayyana cewa, “Amurka ta ɗauki mataki mara son Rai, na cewa ‘ samun ribar kasuwanci sai an yi zamba’ wanda ya kai ga kai wa ƙasashen Afrika haraji mai yawa, wanda ya saɓa wa ƙa’idojin WTO na bayar da kulawa ta musamman ga ƙasashen masu tasowa.”

China
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa
  • Abubakar Sulaiman
    Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila
  • Abubakar Sulaiman
    Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?

Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
sikila

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 26, 2026
makarfi

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.