ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

China Na Neman Ƙasashe Su  Haɗe Wa Amurka Kai Sakamakon Ƙarin Haraji

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
China

Jakadan ƙasar China a Nijeriya, Yu Dunhai, ya yi kira ga al’ummar duniya da su haɗa kai don yaƙi da yawan haraji da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ke ƙara wa ƙasashe da dama, yana gargadin cewa wannan mataki na iya janyo koma baya ga tattalin arziƙin duniya tare da illoli masu tsanani musamman ga Afrika.

A lokacin taron manema labarai da ya yi a Abuja ranar Juma’a, jakadan ya jaddada cewa matakan Amurka sun take haƙƙin ƙasashe da dama, sun saɓa dokokin yarjejeniyar kasuwanci ta duniya (WTO), suna kuma kawo matsala ga tsarin ciniki na ƙasa da ƙasa da zai iya haifar da rushewar tsarin tattalin arzikin duniya.

  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China
  • EFCC Ta Gurfanar Da Ɗan China A Kotu Kan Bayar Da Bayanan Ƙarya

Ya bayyana cewa, “Al’ummar duniya dole ne su haɗa kai su yaƙi wannan zalunci domin kare abubuwan da suka shafi al’umma baki ɗaya. Ya ƙalubalanci amfani da haraji a matsayin abin cin fuska ko tirsasawa daga Amurka da nufin tsayawa kan daidaito da gaskiya da kuma adalci.”

Shugaban Amurka ya ƙara tsananta haraji ga ƙasashe da dama, China tana cikin waɗanda suka fi fuskantar ƙarin haraji mai yawa, da 145% na kayan China da sazu shiga kasuwar Amurka, yayin da Beijing ta mayar da martani da haraji na 125% kan kayan Amurka.

ADVERTISEMENT

Ƙasashe da dama ciki har da Tarayyar Turai (EU) sun ɗora haraji a kan Amurka, wanda ya sa gwamnatin Trump ta dakatar da aiwatar da sabon tsarin haraji na kwanaki 90 domin buɗe damar tattaunawa.

Jakada Dunhai ya ƙara da cewa wannan tsarin haraji yana keta ƙa’idar tattalin arziƙi da dokokin kasuwanci, da ƙin la’akari da cewa Amurka ta daɗe tana cin riba daga kasuwanci na ƙasa da ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

“Amfani da haraji a matsayin makami don matsin lamba da son rai yana nuni da tsarin siyasa na rashin haɗin kai da kare tattalin arziƙi da kuma zambar tattalin arziƙi. Wannan ba abu ne na adalci ba ko mai kyau – yana nufin zaman ‘Amurka da tafi kowa’ da kuma ƙaruwar ƙarfin Amurka,” in ji shi.

Jakadan ya kuma yi gargadi cewa ƙasashe masu tasowa za su fi shan wahala daga wannan tsarin haraji, kuma hakan zai fi cutar da ƙasashen Afrika, ciki har da Nijeriya.

Ya bayyana cewa, “Amurka ta ɗauki mataki mara son Rai, na cewa ‘ samun ribar kasuwanci sai an yi zamba’ wanda ya kai ga kai wa ƙasashen Afrika haraji mai yawa, wanda ya saɓa wa ƙa’idojin WTO na bayar da kulawa ta musamman ga ƙasashen masu tasowa.”

China
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja
  • Abubakar Sulaiman
    Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Abubakar Sulaiman
    Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya
  • Abubakar Sulaiman
    Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

MASU ALAKA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kasashen Ketare

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

May 30, 2026
Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu

May 30, 2026
Next Post
Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?

Mene Ne Shirin Nukiliya Na Iran Kuma Me Amurka Ke So Ta Yi?

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Na Harkokin Kasuwanci

June 5, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Karin Bayani Game Da Ziyarar Da Xi Zai Yi A Koriya Ta Arewa

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026
An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

An Fitar Da “Rahoton Yanayin Muhalli Na Kasar Sin Na 2025”

June 5, 2026
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Sace Janar Rabe Abubakar A Katsi

June 5, 2026
Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

Labarin Yin Yuzhen: Sin Tana Hadin Gwiwa Da Ketare Don Cika Alkawarin Kiyaye Muhallin Duniya

June 5, 2026
Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

Kiwon Shanu A Titunan Abuja Barazana Ne Ga Tsaron Nijeriya —Wike

June 5, 2026
Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos

Shugaban Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Laos

June 5, 2026
Shugaban Kasar Laos: Layin Dogo Na Sin Da Laos Ya Sa Burin Al’Ummar Laos Ya Zama Gaskiya

Shugaban Kasar Laos: Layin Dogo Na Sin Da Laos Ya Sa Burin Al’Ummar Laos Ya Zama Gaskiya

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.