ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hukuncin Kotun Koli Ya Kara Dagula Rikicin Shugabanci A PDP Da LP

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Kotun

Duk da hukuncin kotun kolin Nijeriya, rikicin shugabanci da ya dabaibaye jam’iyyar PDP da LP ya kara kamari, a halin da ake ciki har yanzu jam’iyyun guda biyu sun gaza magance rikicin shugabanci.

Duk da cewa shugabannin jam’iyyun biyu sun yaba da hukuncin kotun koli wanda a cikin hukunce-hukuncen daban-daban, har yanzu jam’iyyun biyu ba su sami masalaha ba game da warware rikicin cikin gida a tsakaninsu.

  • Manchester Ta Kai Zagayen Semi Final A Europa Bayan Doke Lyon
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 157, Sun Ƙwato Bindigu Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Yayin da jam’iyyar PDP ke fama game da rikicin sakataren jam’iyyar na kasa, inda jam’iyyar LP ke fama da rikicin shugabanta na kasa.

ADVERTISEMENT

Mutane uku na ikirarin zama shugabannin LP, yayin da Sanata Samuel Anyanwu da Hon. Sunday Udeh-Okoye ke fafatawa kan wane ne ainihin sakataren PDP na kasa.

A cikin LP, Kwamared Julies Abure ya ci gaba da rike sakatariyar jam’iyyar, yayin da Sanata Nenadi Usman da Lamidi Apapa suma ke ikirarin zama shugabannin jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Wata majiya ta ce PDP na cikin mawuyacin hali da kuma rashin tabbas a harkokinta wanda ya tilasta jinkirta taron shiyya da aka shirya gudanarwa a karshen makon da ya gabata.

Wata majiya ta ce hukuncin da kotun koli ta zartar akwai rikitarwa saboda an gwama siyasa a ciki.

Amma sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba ya fada a wata hira kan cewa hukuncin kotun koli a bayyane yake kuma yana da fa’ida ga gudanar da jam’iyyar a kasar, ya kara da cewa an ba da ikon magance matsalolin da ke tattare da rikice-rikicen da za su iya shafi masu rike da mukaman jam’iyyar.

Ya ce abin da kotun ta yanke hukunci shi ne cewa dole ne a warware duk wani abu da ya shafi matsayi na jam’iyya ta hanyar tsarin cikin gida na jam’iyya, sannan kotun ta ce ba za ta yi katsalandan ga al’amuran jam’iyyu ba kamar yadda dokoki da ka’idoji suka bayyana.

Ya ce PDP ba ta cikin wani mawuyacin hali game da hukuncin, ya kara da cewa tsarin cikin gida na jam’iyyar zai yanke shawara tare da samar da mafita.

Yayin da PDP tana cikin mawuyacin hali saboda jinkirin warware matsayin sakataren jam’iyyar na kasa, al’amura na kara tabarbarewa a LP. A makon da ya gabata ne bangare uku suke ikirarin zama shugabannin jam’iyyar na kasa.

Julius Abure, Nenadi Usman da Lamidi Apapa sun ci gaba ikirarinsu na zama a matsayin shugabancin jam’iyyar, duk da cewa sakataren yada labarai na kasa, Obiora Ifoh, ya bayyana cewa wadanda ke fafatawa da Abure suna yin was an kwaikoyo ne kawai.

A cewarsa, a yayin da kotun koli ta fadi karara cewa ba ta da iko a kan lamarin da ya shafi rikicin cikin gida na jam’iyya kuma ta mayar da iko ga tsarin jam’iyyar, wasu mambobin jam’iyyar suna yin wasan kwaikwayo ta hanyar zuwa ofishin hukumar zabe ta kasa, lamarin da ya ce ba shi da tasiri.

Ya ce hukuncin kotun koli ya yi watsi da batun shugabancin jam’iyyar tare da soke hukuncin kotun daukaka kara, har ma ba ta tabbatar da wani mutum a matsayin shugaban jam’iyyar ba.

“Abin da wannan ke nufi shi ne, an mayar da jam’iyyar zuwa matsayi na farko. Kuma Abure ya kasance shugaban jam’iyyar na kasa har tsawon lokacin da wa’adinsa ya kare,” in ji Ifoh.

Mai magana da yawun jam’iyyar ya gargadin Sanata Nenadi Usman da sauran masu adawa da Abure cewa kar su yaudari ‘yan Nijeriya da fassarar da ba daidai ba game da hukuncin kotun koli.

Kotun
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Kotun
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu

Kasar Sin Ta Mallaki Tasoshin Fasahar 5G Miliyan 4.4 A Halin Yanzu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.