• English
  • Business News
Monday, June 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bude Kashi Na Uku Na Canton Fair Karo Na 137 

by Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
An Bude Kashi Na Uku Na Canton Fair Karo Na 137 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Alhamis 1 ga watan Mayu ne aka bude kashi na uku na bikin baje kolin kayayyakin shige da fice na kasar Sin wanda aka fi sani da Canton Fair karo na 137, inda kamfanoni 12,043 ke halarta, tare da mayar da hankali a kan taken bikin mai lakabin “Rayuwa Mai Kyau”. 

 

Kashi na uku na bikin Canton Fair na bana ya kunshi sassa biyar tare da wuraren baje koli guda 21, wadanda suka hada da na kayan wasan yara da kayan jarirai, da tufafi, da kayan gida, kayan rubutu da karatu, da na kiwon lafiya da kuma na nishadi.

  • Kasar Sin Ta Yi Kiran Kawar Da Makaman Nukiliya Bisa Tsarin Tsaro Na Bai Daya
  • Nijeriya Za Ta Karɓi Bakuncin Gasar Karatun Alƙur’ani Mai Girma Ta Duniya

Bisa zurfafa bincike kan bukatun masu sayayya, kamfanoni masu baje kolin hajojinsu, sun kaddamar da karin samfuran kayayyaki na musamman masu inganci, inda ta hakan suka zo da wani sabon salo na kyautata rayuwa da ba da gudummawa ga habaka samar da rayuwa mai inganci.

 

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan

An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

Cibiyar cinikayyar kasashen waje ta kasar Sin, mai shirya bikin, ta ba da sanarwar cewa, baya ga wuraren baje kolin da suka shafi farfado da yankunan karkara da za a ba su rumfuna kyauta, sauran masu baje kolin kayayyakin da ake fitarwa zuwa kasashen waje su ma za a rage musu kudaden rumfunansu da kashi 50 cikin dari a wajen bikin Canton Fair karo na 137.

 

Ana gudanar da bikin Canton Fair karo na 137 ne a matakai uku, daga ranar 15 ga Afrilu zuwa 5 ga Mayu. Kashi na farko da na biyu sun jawo hankulan masu sayayya fiye da 220,000 daga kasashe da yankuna 219 na duniya, inda suka kafa sabon tarihi a lokaci guda.

 

Wannan ya nuna yadda kasuwancin kasashen waje na kasar Sin ya tsaya kyam da kafafunsa tare da karin kuzari, kana ya kara wa kamfanoni kwarin gwiwar yin bincike kan yadda za su ci gajiyar kasuwanni daban daban. (Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Sin Ya Yi Tir Da Matakan Amurka Na Karin Harajin Kwastam A Taron WTO

Next Post

Ma’aikata Sun Kauracewa Fareti, Sun Gudanar Da Taron Goyon Baya Ga Dakataccen Gwamnan Ribas

Related

Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan

1 hour ago
An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

4 hours ago
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

22 hours ago
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

23 hours ago
Dan Asalin Tudun Loess
Daga Birnin Sin

Dan Asalin Tudun Loess

24 hours ago
Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba
Daga Birnin Sin

Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

1 day ago
Next Post
Ma’aikata Sun Kauracewa Fareti, Sun Gudanar Da Taron Goyon Baya Ga Dakataccen Gwamnan Ribas

Ma'aikata Sun Kauracewa Fareti, Sun Gudanar Da Taron Goyon Baya Ga Dakataccen Gwamnan Ribas

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

June 16, 2025
Hauhawar Farashi Ya Sauka Zuwa Kashi 22.9 A Watan Mayun 2025

Hauhawar Farashi Ya Sauka Zuwa Kashi 22.9 A Watan Mayun 2025

June 16, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan

Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan

June 16, 2025
An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

An Daddale Tarin Yarjejeniyoyi Yayin Taron Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka

June 16, 2025
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Jigila Kai Tsaye Zuwa Sin Da Indiya

FCCPC Ta Sammaci Air Peace Kan Rashin Maido Da Kuɗin Tikitin Jirgin Da Aka Soke Tafiyarsa

June 16, 2025
Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya

June 16, 2025
Dan Nijeriya Lookman Na Kan Gaba Wajen Lashe Kyautar Gwarzon Kwallon Kafa Na Afrika Ta Bana

Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman

June 16, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya

June 16, 2025
IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 

June 16, 2025
Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas

June 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.