• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ba Za Ta Cimma Nasara Ta Hanyar Yakin Cinikayya Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Amurka

Shugabar sabon bankin samar da ci gaba na NDB Dilma Rousseff, ta ce kokarin da kasar Amurka ke yi na warware tarin matsalolinta, da matakan babakere da kudin kasar dala ta haifar ba zai haifar da da mai ido ba. Maimakon hakan, matakin zai kara illata Amurkan ne kawai.

 

Rousseff, wadda ta bayyana hakan yayin wata zantawa da kafar CMG ta kasar Sin, ta ce matakan kakaba haraji da Amurka ta ayyana a ranar 2 ga watan Afrilun da ya shude, sun sanya kasashe da dama fara jingine dalar Amurka, sai dai kuma Amurka ta karkata ga zargin wasu kasashe da laifin hakan. Ta ce kasuwar hada-hadar kudade ta duniya ta shiga yanayi na tangal-tangal da ba ta ga irinsa ba cikin gomman shekaru, kana darajar dalar Amurka ta fadi, su ma kasuwannin hada-hadar hannayen jari sun gamu da koma-baya, yayin da takardun lamani na baitulmalin Amurka suke fada yanayi na rashin tabbas. Rousseff ta yi imanin cewa, gibin cinikayya da Amurka ke fama da shi a halin yanzu, ba shi da nasaba da batun haraji.

  • Dakataccen Gwamnan Ribas Ya Dawo Daga Hutun Makonni Biyu A Kasar Waje
  • Bayan Fara Binciken $2.96bn, An Samu N80bn A Asusun Tsohon Daraktan Kamfanin NNPCL

A nasa bangare, tsohon ministan kudin kasar Faransa, yayin gwamnatin Charles de Gaulle mista Valéry Giscard d’Estaing, ya ce dalar Amurka ta samu matukar fifiko kan sauran kudaden musaya, wanda hakan ya sa kasashe da dama mika kudadensu na asusun ajiya ga Amurka, ba tare da la’akari da tsada ko kudin ruwa ba. Ya ce bisa hakan ne Amurka ta samu damar juya kudaden ajiyar ba tare da biyan kudin ruwa na a-zo-a-gani ba. Kuma hakan na nufin Amurka na da ikon kashe kudade ba kaidi, tare da dorawa kanta tarin bashi.

 

LABARAI MASU NASABA

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

A yanzu kuma, Amurka na son kawar da dimbin gibin kudaden asusunta, ta hanyar amfani da kare-karen haraji. A baya Amurka ta yi kokarin hakan ba tare da cimma nasara ba, kuma a yanzu ma hakan ne zai sake faruwa. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Daga Birnin Sin

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Next Post
‘Yan Ta’adda Sun Kashe Laftanar Din Soja A Yobe

ISWAP Sun Kai Hari Sansanin Sojoji A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.